ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fayemi Ga Ganduje: Ka Rika Fada Wa Tinubu Gaskiyar Halin Da APC Ke Ciki

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Fayemi

Tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Dakta Kayode Fayemi, ya bukaci shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, da ya fito fili ya fada wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ainihin halin da ake ciki a APC, ba bayanin da yake samu a cikin fadar shugaban kasa ba.

Fayemi wanda ya kasance tsohon shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya (NGF), ya yi wannan kira ne ga Ganduje a yayin kaddamar da wani littafi mai suna “Yadda APC ke gudanar da siyasarta”, wanda tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar APC na kasa na yankin  Arewa maso yamma, Salihu Mohammed Lukman ya rubuta, da ya gudana a Abuja.

  • Kamfanonin Jamus 22 Za Su Zuba Jarin Fam Biliyan 3 A Nijeriya
  • Kwankwaso A Sikeli Bayan Hukuncin Kotun Koli

Taron ya samu halartar fitattun jagororin jam’iyyar APC da suka hada da Ganduje da tsaffin shugabannin jam’iyyar APC na kasa, Adams Oshiomhole da Cif Bisi Akande da wakilan mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo da na shugaban majalisar wakilai, Tajuddeen Abbas da mambobin kwamitin gudanarwa na kasa da sauransu.

ADVERTISEMENT

Fayemi ya ce, “Na yi farin ciki da shugaban jam’iyyarmu ya zo wannan wuri. Wannan jam’iyyar bai kamata ta zama ‘yar kallo ba wajen tsara manufofin gwamnati. Ya kamata jam’iyya ta zama ita ce za ta tsara manufofin gwamnati. Ya kamata wannan gwamnati da dinga bin manufofin jam’iyya wajen aiwatar da tsare-tsarenta wadanda suka dace domin kawo wa al’umma sauki, ba wai abin da shugaban kasa yake ji a fadar shugaban kasa ba.

“Dukkanmu mun taba rike mukamin gwamnati kuma mun san yadda al’amura suke. Na yi farin ciki da shugabanmu ya tabbatar da cewa zai karanta wannan littafin. Kamata ya yi ya zama wajibi a karanta wa dukkan ‘ya’yan kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC da shugabanni a matakin jiha da na unguwanni domin mu fara aikin sake gina jam’iyyarmu wadda na yi imanin Dakta Abdullahi Umar Ganduje zai jajirce a kai.”

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

A nasa jawabin, Ganduje ya ce jam’iyyar APC na bukatar a samar da tsari mai kyau tare da mayar da hankali wajen biyan bukatun al’ummar Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025
Tambarin Dimokuradiyya

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Next Post
Sauran Gwarazan Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP A 2023

Sauran Gwarazan Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP A 2023

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.