• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

by yahuzajere
2 years ago
ACG James Sunday

Gwambawa a karkashin Kungiyar Tsofaffin Daliban Makarantar Sakandaren Kimiyya ‘yan ajin 1984 da kuma Kungiyar ‘Yan Ajin Digiri na Biyu a Fannin Nazarin Harkokin Kasashen Waje da Difilomasiyya (MIAD) da suka kamala a 2008, sun shirya wa ACG James Sunday kwarya-kwaryan bikin taya murnar samun karin girman a Hukumar Shige da Fice ta Kasa (NIS).

James Sunday ya samu Karin girma daga Kwanturola na Jiha zuwa mukamin Mataimakin Kwanturola Janar (ACG)

An gudanar da kwarya-kwaryar taron bikin ne a harabar makarantar sakandaren ta kimiyya da ke Gombe a farkon makon nan.

Daruruwan mutane da ‘yan’uwa da abokan arziki da suka halarta, sun yi ta fatan alheri ga babban jami’in tare da addu’ar samun nasara a sabon mukamin nasa.

Da yake Karin bayani ga wakilinmu, ACG James Sunday ya yi godiya ga wadanda suka shirya bikin wanda ya ce saboda kauna ce tsantsa suka yi masa haka, kana ya gode wa Kwanturola Janar ta NIS, CGI Caroline Wura-Ola Adepoju da Ministan Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu bisa tabbatar musu da Karin girma kana ya nanata kudirinsa na ci gaba da aiki tukuru domin sauke nauyin da tsarin mulkin kasa ya dora musu.

LABARAI MASU NASABA

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

  • Buhari Zai Halarci Taron Tattaunawa Da Kungiyar Tuntuba Ta Katsina
  • Tinubu Ga Gwamnoni: Dole Ne Mu Tabbatar Da Zaman Lafiya A Nijeriya

 

ACG James Sunday wanda ya kammala makarantar sakandaren ta Gombe kuma daga bisani ya halarci Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Gombe inda ya kammala tare da samun lambar yabo a matsayin dalibi mafi kwazo a shekarar 1987, har ila yau ya halarci Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kaduna tare da nazartar Ilimin Fasahar Masana’antu.

Ya fara aiki da Hukumar Shige da AFice ta Kasa a 1989 inda ya halarci makarantar horaswa ta jami’an hukumar da ke Kano tare da kammalawa da samun lambobin yabo da suka hada ta minista da kuma ta darakta wanda ake bai wa jami’I mafi kwazo.

Shi ne ya zama jami’in hulda da jama’a na farko (PRO) a NIS da ya fara rike matsayin daga matakin babban ofishin jiha a Jihar Ribas, sai kuma ya zama na ofishin babbar shiyya ta Zone B mai shalkwata a Kaduna daga bisani kuma ya zama Babban Jami’in Hulda da Jama’ar ta NIS baki daya a shalkwatarta da ke Abuja

Shi ne ya fara zama jami’in sashen aikin hadin gwiwa a tsakanin Rundunar ‘Yansandan Duniya da NIS wanda sashen ne ya samar da hanyoyin da hukumomin biyu suka kafa sashen sadarwa a shalkwatar ‘yansanda ta kasa daga bisani aka yi nasarar kaddamar da manhajar rundunar ‘yansandan duniya da ke aiki dare da rana kullum. Wannan ya taimaka gaya wajen hadin gwiwar aiki a tsakanin Nijeriya da ‘yansandan duniya musamman a tsakanin hukumomin tsaro da NIS ke jagorantarsu a wannan fannin.

Bugu da kari, ACG James Sunday, ya zama jami’i na farko da aka nada mai bai wa ministan cikin gida shawara a kan harkar tsaro a lokacin da ake tsananin bukatar basirar wani kwararre ta fuskar tattara bayanan sirri domin magance fashe-fashen gidajen yari da kuma yin gyaran fuska ga ayyukan gidajen yari. Ya yi wannan aikin ne a matsayin jami’in da aka ba da aron sa.

Yanzu haka, ACG James Sunday, shi ne babban jami’i shalkwatar NIS ta shiyyar Zone C mai kula da arewa maso gabas da ta kunshi Jihohin Adamawa, Bauhci, Borno, Gombe, Filato da kuma Yobe,

ACG James Sunday jami’i ne da ya yi shuhura a fannin aikin yada labarai da sadarwa wanda ake matukar girmamawa a gamayyar hukumomin tsaro ta FOSSRA da ta kunshi daukacin jami’an hulda da jama’a. Har ila yau, marubuci ne da ya wallafa littafai, da Makalu, kana yana da sha’awar wasan kwallon dawaki da na golf, sannan mutum ne mai son Ubangiji, magidanci da yake da aure da kuma ‘ya`ya masu albarka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri
Labarai

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar
Manyan Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
Next Post
Ta Shiga Caji Ofis Ta Harbe Saurayinta Dan Sanda Har Lahira 

Ta Shiga Caji Ofis Ta Harbe Saurayinta Dan Sanda Har Lahira 

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.