ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Halarci Taron Tattaunawa Da Kungiyar Tuntuba Ta Katsina

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Buhari

Kungiyar tuntuba ta “Katsina Consultative Forum” za ta shirya wani taron tattaunawa a kan matsalar shaye-shaye da suke yi wa zaman lafiya Jihar Katsina da Kasa barazana wanda kuma ake sa ran cewa tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari na daga cikin manyan baki da za su halarci wannan taro a Katsina.

Shugaban Kungiyar Tuntuba na Jihar Katsina, Alhaji Aliyu Abubakar Danmusa ya bayyana haka a lokacin wani taron manema labarai wanda ya yi karin haske kan yadda taron zai kasance da kuma dalilin da ya sa suka sauki matsalar shaye-shaye a matsayin batun da za su tattauna a kansa.

  • Gwamna Bago Ya Yi Watsi Da Rahoton Haramta Sayar Da Giya A Neja
  • Gwamnatin Zamfara Ta Rufe Kasuwannin Shanu 11 Saboda Matsalar ‘Yan Bindiga A Jihar

Ya kara da cewa an gayyato masana daga kowane bangare domin baje kolin hanyoyin da za a yi amfani da su domin sannin hanyar da za a tunkari wannan annoba ta sha da fataucin miyagun kwayoyi da suke haifar da abubuwa marasa kyau a cikin al’umma.

ADVERTISEMENT

Haka kuma ya yi bayanin cewa ba harkar shan kwayoyi ba ce kadai matsala ba, yana mai cewa sannu a hankali za su rika daukar matsalolin daya bayan daya domin tattaunawa akan su tare da lalubu hanyoyin da gwamnatin da kuma masu ruwa da tsaki za su bada gudunmawa domin magance su.

“Mun lura cewa matsalar kwaya, ita ce ke jagoranci zuwa ga aikata manyan laifufuka da suka hada shiga harkar ‘yan bindiga da fashi da makami da fyade da sauran manyan laifufuka, saboda haka dole mu hada hannu domin tunkarar wannan matsala baki dayanmu” in ji shugaban.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Alhaji Aliyu Abubakar ya kara da cewa wannan taron zai samu tagomashi daga masana da masu ruwa da tsaki da za su baje kolin basirarsu a kan wannan matsala, mutane irin su Dakta Usman Bugaje masanin magunguna da siyasa da shugabar hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta jihar Katsina, Dakta Asma’u Abdulkadir da kuma mai baiwa gwamnan Katsina shawara akan hana sha da fataucin kwayoyi na da cikin manyan baki a wajen taron

A cewarsa halartar manyan baki irin su tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda da Sarakunan Katsina da Daura na daga cikin abubuwan da za su karawa taron armashi da fatan cewa za a yi abainda ya kamata akan wannan matsala.

Haka kuma ya yi bayanin cewa an gayyaci matasa wadanda sune wannan matsala ta shafa kai tsaye musamman daliban jami’o’i da matasa masu yi wa kasa hidima da kungiyoyin da ba na gwamnati ba.

Wannan taro kamar yadda shugaban wannan kungiya ya bayyana za a gudunar da shi a ranar 31 ga watan Disamba, 2023 a baban dakin taron na masaukin shugaban kasa da ke fadar gwamnatin Jihar Katsina.

Buhari
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.