ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Halarci Taron Tattaunawa Da Kungiyar Tuntuba Ta Katsina

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Buhari

Kungiyar tuntuba ta “Katsina Consultative Forum” za ta shirya wani taron tattaunawa a kan matsalar shaye-shaye da suke yi wa zaman lafiya Jihar Katsina da Kasa barazana wanda kuma ake sa ran cewa tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari na daga cikin manyan baki da za su halarci wannan taro a Katsina.

Shugaban Kungiyar Tuntuba na Jihar Katsina, Alhaji Aliyu Abubakar Danmusa ya bayyana haka a lokacin wani taron manema labarai wanda ya yi karin haske kan yadda taron zai kasance da kuma dalilin da ya sa suka sauki matsalar shaye-shaye a matsayin batun da za su tattauna a kansa.

  • Gwamna Bago Ya Yi Watsi Da Rahoton Haramta Sayar Da Giya A Neja
  • Gwamnatin Zamfara Ta Rufe Kasuwannin Shanu 11 Saboda Matsalar ‘Yan Bindiga A Jihar

Ya kara da cewa an gayyato masana daga kowane bangare domin baje kolin hanyoyin da za a yi amfani da su domin sannin hanyar da za a tunkari wannan annoba ta sha da fataucin miyagun kwayoyi da suke haifar da abubuwa marasa kyau a cikin al’umma.

ADVERTISEMENT

Haka kuma ya yi bayanin cewa ba harkar shan kwayoyi ba ce kadai matsala ba, yana mai cewa sannu a hankali za su rika daukar matsalolin daya bayan daya domin tattaunawa akan su tare da lalubu hanyoyin da gwamnatin da kuma masu ruwa da tsaki za su bada gudunmawa domin magance su.

“Mun lura cewa matsalar kwaya, ita ce ke jagoranci zuwa ga aikata manyan laifufuka da suka hada shiga harkar ‘yan bindiga da fashi da makami da fyade da sauran manyan laifufuka, saboda haka dole mu hada hannu domin tunkarar wannan matsala baki dayanmu” in ji shugaban.

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

Alhaji Aliyu Abubakar ya kara da cewa wannan taron zai samu tagomashi daga masana da masu ruwa da tsaki da za su baje kolin basirarsu a kan wannan matsala, mutane irin su Dakta Usman Bugaje masanin magunguna da siyasa da shugabar hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta jihar Katsina, Dakta Asma’u Abdulkadir da kuma mai baiwa gwamnan Katsina shawara akan hana sha da fataucin kwayoyi na da cikin manyan baki a wajen taron

A cewarsa halartar manyan baki irin su tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda da Sarakunan Katsina da Daura na daga cikin abubuwan da za su karawa taron armashi da fatan cewa za a yi abainda ya kamata akan wannan matsala.

Haka kuma ya yi bayanin cewa an gayyaci matasa wadanda sune wannan matsala ta shafa kai tsaye musamman daliban jami’o’i da matasa masu yi wa kasa hidima da kungiyoyin da ba na gwamnati ba.

Wannan taro kamar yadda shugaban wannan kungiya ya bayyana za a gudunar da shi a ranar 31 ga watan Disamba, 2023 a baban dakin taron na masaukin shugaban kasa da ke fadar gwamnatin Jihar Katsina.

Buhari
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Next Post
Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.