• English
  • Business News
Monday, June 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi

by Bello Hamza
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanarwar da Gwamnatin tsohon shugaba Muhammadu Buhari ta sauya wasu takardun kudi tare da fara bayarwa daga ranar 15 ga Dismba, 2022 zuwa 31 ga Janairu, 2023, na daga cikin abubuwan da suka fi daukar hankali a 2023 saboda yadda lamarin ya shafi rayuwar ‘Yan Nijeriya.

Duk da shiga maganar da Majalisar Kasa ta yi na neman Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya tsawaita wa’adin da ya bayar na daina karbar tsofaffin takardar kudin 1000, 500 da 200, Babban Bakin ya ce ba za a kara koda minti daya ba a wa’adin da aka sanya na ranar 31 ga watan Janairu 2023, inda hakan ya sa ‘yan Nijeriya cikin dimuwa. Amma daga bisani da gwamnati ta ji matsin lamba, sai ta kara wa’adin zuwa 11 ga Fabrairu, 2023.

  • Harin Filato: Gwamnati Ba Za Ta Huta Ba Har Sai An Hukunta Maharan – Shettima 
  • NAF Ta Lalata Haramtattun Wuraren Tace Mai Guda 6 A Ribas 

Al’umma sun shiga cikin dimuwa da fargaba. Karancin takardun sabbin kudin da rige-rigen sauyawa a bankuna ya kara haifar da wahalhalu ga ‘yan kasa. Masana sun bayyana cewa, CBN ya samar da sabbin kudin ne na Naira Biliyan 200 kuma abin da ake bukata ya kai fiye da Naira Tiriliyan 3.1 abin da ya sa masana ke ganin shi ne babban dalilin karancin sabbin kudaden.

Masu harkar canjin kudin sun mayar da harkar canjin kasuwanci inda aka rika sayar da sayar da sabbin a unguwar zone 4 da ke babba birnin tayarra Abuja.

Wani karin abin haushi game da canjin kudin shi ne, hanyoyin da ake hada-hadar kudin ta intanet duk sun rika toshewa ta yadda abin ya zama kasada, imma kudin da aka tura ya tafi ko ya salwanta.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

Ba a wannan karon aka fara canza fasalin kudi a Nijeriya, shugaba Buhari a lokacin da ya jagorancin Nijeriya a matsayin soja a shekara 1983 ya yi canjin kudi wanda ‘yan Nijeriya da dama suka tafka asara sabosa kasa cimma wa’adin mayar da tsofaffin kudin zuwa banki wannan ya sa wadanda suka san irin dambarwar da aka fuskanta a waccan lokacin suka shigta dimuwa da fargabar halin da za a iya shiga in har wa’adin ya kulle mutum bai kai kudinsa banki ba.

Canjin kudi na wannan karon ya zo ne ana tsakiyar hada-hada da gangamin siyasar 2023, kuma kowa yana sane da cewa, harkar siyasa a kasar nan abu ne da ya yake tafiya da kudi, ma’ana iya kudin ka iya shagalin ka

Dimuwa da tashin hankalin da mutane suka shiga sun sa wasu na ikirarin ba za su zabi jam’iyya mai mulki ba, abin da ya sa dan takarar shugaban kasa a jam’iyya mai mulki ta APC Asiwaju Biola Ahmed Tinubu ya bara, ya yi korafin cewa, an kikiro da lamarin tun da farko don kawo masa cikas a yunkurinsa na zama shugaban Nijeriya.

Masu lura da al’amurran yau da kullum sun bayyana cewa, jifar tawagar shugaban kasa a yayin da ya kai ziyara garin Katsina don kaddamar da wasu ayyukan raya kasa da kuma ihun da aka yi a ziyarar kaddamar da wasu ayyukan raya kasa a Jihar Kano, inda wasu yara suka yi jifa da furuce-furucen “Ba ma yi! Bama son canji, da sauransu”, tabbas a bayyane yake cewa, al’amarin canjin ya kara wa gwamnatin Shugaba Buhari bakin jinni.

A wata sabuwa kuma, da yake bayani a wani zauren tattauna wanda wasu shaharrun Lauyoyi da ‘yan Jarida ke gabatarwa a shafin intanet, Manjo Hamza Al-mustapa (Mai Ritaya) ya ce, canjin kudn da aka yi ba komai ba ne illa damfara, yana mai cewa, “419 (Damfara) aka shirya domin a wahalar da ‘yan Nijeriya, idan kuma Emifiele  ya isa, ko shi, ko mukarrabansa su fito fili su karyata in ban tona asiri ba” in shi ji.

Haka kuma Gwamnan JIhar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa, akwai wasu a fadar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da suke neman kayar da dan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu.

Yanzu haka dai tsohon Gwamnan CBN, Godwin Emefiele na fuskantar tuhuma daban-daban a kan badakalar kudi a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bankwana Da 2023: Radadin Cire Tallafin Mai

Next Post

Bashin Ilimi Ga Daliban Nijeriya: Manufar Da Ba Ta Da Kyakkyawar Manufa

Related

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

5 hours ago
Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya
Manyan Labarai

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

14 hours ago
Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027
Manyan Labarai

Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

19 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa
Manyan Labarai

NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

1 day ago
Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
Manyan Labarai

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

2 days ago
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
Manyan Labarai

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

2 days ago
Next Post
Bashin Ilimi Ga Daliban Nijeriya: Manufar Da Ba Ta Da Kyakkyawar Manufa

Bashin Ilimi Ga Daliban Nijeriya: Manufar Da Ba Ta Da Kyakkyawar Manufa

LABARAI MASU NASABA

Dan Nijeriya Lookman Na Kan Gaba Wajen Lashe Kyautar Gwarzon Kwallon Kafa Na Afrika Ta Bana

Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman

June 16, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

June 16, 2025
IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

June 16, 2025
Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

June 16, 2025
Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

June 15, 2025
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

June 15, 2025
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

June 15, 2025
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

June 15, 2025
Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

June 15, 2025
Dan Asalin Tudun Loess

Dan Asalin Tudun Loess

June 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.