ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bashin Ilimi Ga Daliban Nijeriya: Manufar Da Ba Ta Da Kyakkyawar Manufa

by Alhaji Adamu Rabiu
3 years ago
Ilimi

LABARAI MASU NASABA

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

A kwanakin baya ne aka sanya hannu kan dokar bayar da bashin dalibai da kuma yadda aka ware kudi kimanin naira biliyan hamsin, a cikin kasafin kudin shekarar 2024, domin bayar da rancen dalibai. Duk da dai, manufofin da ke bayan kudirin na da kyau.

Kazalika, nazari ya tabbatar da cewa, manufar ba za ta haifar da da mai ido ba, yayin da kuma tunani da hasashe ya nuna rashin adalci da inganci da kuma mummunar manufa ga jin dadin daliban Nijeriya da sauran ‘dan kasa.

  • Sin Za Ta Dauki Matakan Da Suka Dace Kan Kamfani Da Wasu Mutanen Amurka Da Suka Shafi Batun Xinjiang
  • Kasar Sin Ta Ware Yuan Miliyan 400 Don Taimakawa Wadanda Bala’in Girgizar Kasa Ta Shafa A Gansu Da Qinghai

Sharuddan Bayar Da Bashin

Uku daga cikin sharuddan samun wannan rance na da matukar tsauri, wanda zai iya iyakancewa maimakon karfafa masu neman izini. Wadannan su ne na daya, mai garantin ma’aikacin gwamnati mai mataki na 12 ko kuma mutum mai daraja, yanzu mutum nawa ne ke da ma’aikaci mai daraja 12 a cikin danginsu ko kuma wani mutum mai daraja wanda kuma yake son daukar irin wannan nauyi?

Na biyu, dalibin da zai rattaba hannu a kan alkawarin biyan bashin a cikin wani kayyadadden lokaci, wa ke da tabbacin gobe idan aka yi la’akari da manufofin da gwamnati ke furtawa babu zato babu tsammani?

Na uku, dole ne dalibai su bi dukkanin wasu sharudan da hukumar lamuni ta dalibai za ta gindaya musu, wannan yana nuni ne da canza “dokokin bayar da bashin rana tsaka”. Kar a yi maganar cikas na ofisoshi da ke da alaka da kowane talafi na  gwamnati da yanayin siyasar Nijeriya.

Kalubalen Da Dalibai Da Iyaye Za Su Fuskanta

Duk da makudan kudaden da aka ware, matsalolin da za a fuskanta wajen samun wannan lamuni na da matukar yawa. Bugu da kari, ka’idojin da aka gindaya na nuna cewa, bashin na da  riba a cikinsa.

Damar Da Aka Rasa Da Manyan Tambayoyi

Biliyan hamsin(50) na da yawa, amma duk na rance ne ko kuma babban kaso ya shafi kayayyakin more rayuwa da suka shafi hukumar bayar da bashin ne? Hakan ya sa ayar tambaya a kan abubuwan da gwamnati ta sa a gaba. Idan manufar ita ce a taimaka wa dalibai don neman ilimi mai zurfi, me zai hana a ware wadannan kudade a matsayin  tallafi maimakon bashi?

Sakamakon Rashin Kishin Kasa

  1. Kamar yadda aka tsara a halin yanzu, rancen yana iya haifar da damuwa game da yiwuwarsa na habaka halin rashin kishin kasa a tsakanin matasa. Don haka, ya kamata gwamnati ta sanya hannun jari a harkar iliminsu a matsayin fifikon kasa, abin bakin ciki shi ne; gwamnati na fuskantar kasadar samar da tsarurraka masu daukar ilimi a matsayin mu’amala, maimakon hada hannun jari a makomar kasa.
  2. Aiwatar da kudirin rancen dalibai, wani lamari ne wanda ke nuni da rashin tausayawa daga bangaren jami’an gwamnati. Wadannan jami’ai, a lokacin karatunsu; sun ci gajiyar tallafin karatu kyauta tare da bayar da tallafin karatu da walwala iri daban-daban. Bambance-bambancen da ke tsakanin abubuwan da suka samu da kuma kalubalen da ke tattare da kudirin rancen daliban; ya sanya ayar tambaya a kan yadda gwamnati ke kokarin kyautata rayuwar al’ummarta.

III. Raba kudade a matsayin rancen dalibai ya bambanta sosai da abubuwan da aka ware a wasu wurare cikin kasafin kudi. Makudan kudaden da aka ware domin sayen Jif-jif, gina wa mataimakin shugaban kasa gida na nuna rashin fifiko da bai dace da ka’idojin mulki ba.

Mu Kwatanta Alfanun Bashi Da Sikolashif Mu Gani:

  1. Rashin Daidaito:
  • Lamunin dalibai zai haifar da cikas ga dalibai masu fama da matsalar tattalin arziki.
  • Sikolashif/tallafin dalibai na makaranta na magance rarrabuwar kawuna ta hanyar bayar da taimakon kudi ba tare da nauyin biyan bashi ba. Wannan yana tabbatar da cewa duk dalibi, ba tare da la’akari da yanayin tattalin arzikinsa ba, na da damar samun ingantaccen ilimi. (Shin wannan bai kamata ya zama ma’auni mafi dacewa ba?)
  1. Ingantaccen Amfani Da Albarkatu:
  • Tsarin lamuni na dalibi, na bukatar ingantaccen kayan aikin gudanarwa, gami da kirkirar hanyoyin bayar da lamuni, bin diddigi da tarawa. Wannan aikin gudanarwa; tabbas zai karkatar da albarkatu daga burin farko na tallafa wa ilimi.
  • Sikolashif ya fi daidaitawa ta fuskar gudanarwa. Kudaden na tafiya ne kai tsaye ga dalibai tare da rage sarkakkiya a tsarin mulki da tabbatar da ingantaccen rabon albarkatu, don neman ilimi.
  1. Karfafa Tattalin Arziki Da Ci Gaban Kasa:
  • Lamunin dalibai zai kawo tsaiko wajen bayar da gudunmawar tattalin arzikin da ‘ƴan kasa masu ilimi za su bayar, don ci gaban kasa domin abin damuwa zai fi yadda za a biya ko kuma kaucewa biyan kudin.
  • Sikolashif/tallafi, wadanda suka kammala karatunsu ba tare da bashi ba sun fi bayar da gudummawa ga ci gaban tattalin arziki ta hanyar kasuwanci, kirkire-kirkire tare da sanya hannun jari a kan lokaci cikin al’ummominsu.

Ina  Mafita?

  1. Gabatar da guraben karo karatu mai inganci, domin kwadaitar da nagartar ilimi, domin zaburar da dalibai su himmatu wajen kara kwazo tare da bayar da gudumawa ga al’umma.
  2. Kara yawan kasafin kudi ga Ilimi tare da karkatar da wani bangare nasa zuwa guraben karo karatu, tallafi da kuma inganta ayyukan ilimi baki-daya.

III.     Hadin gwiwar gwamnati da kanfanoni masu zaman kansu, domin habaka kokarin gwamnatin ta hanyar gabatar da sabbin nau’ikan tallafin kudi.

A karshe:

A cewar Nelson Mandela, “Ilimi shi ne makami mafi karfi, wanda zaka iya amfani da shi don canza duniya baki-daya.”Mu yi amfani da wannan makami cikin hikima da adalci, domin ci gaban al’ummar Nijeriya.

Alhaji Adamu Rabiu ya rubuto daga Kaduna.

Ilimi
Alhaji Adamu Rabiu
+ postsBio
  • Alhaji Adamu Rabiu
    https://hausa.leadership.ng/author/alhaji-adamu-rabiu/
    Hanyoyin Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya
  • Alhaji Adamu Rabiu
    https://hausa.leadership.ng/author/alhaji-adamu-rabiu/
    Rashin Tsaro A Nijeriya: Gazawar Masu Mulki Ce Da Cin Amanar Ƙasa
  • Alhaji Adamu Rabiu
    https://hausa.leadership.ng/author/alhaji-adamu-rabiu/
    ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
  • Alhaji Adamu Rabiu
    https://hausa.leadership.ng/author/alhaji-adamu-rabiu/
    Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar
Bakon Marubuci

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

August 28, 2026
An Kusa Ceto Ɗaliban Neja Da Aka Sace – Ribadu
Bakon Marubuci

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

August 28, 2026
Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya
Bakon Marubuci

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

July 24, 2026
Next Post
Manzancin Annabi (SAW) Da Yadda Allah Ya Yalwata Kirjinsa

Manzancin Annabi (SAW) Da Yadda Allah Ya Yalwata Kirjinsa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.