ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankwana Da 2023: Radadin Cire Tallafin Mai

by Bello Hamza
3 years ago
2023

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Ranar 29 ga watan Mayun 2023, da aka rantsar da Asiwaju Bola Tinubu a matsayin Shugaban Nijeriya na 16, za ta ci gaba da kasancewa a cikin tarihi bisa yadda sanarwar da sabon shugaban ya yi na cire tallafin mai za ta ci gaba da kai-komo a zukatan ‘Yan Nijeriya musamman wadanda ke matukar jin radadin abin.

Duk da yake Tinubu ya yi bayanin cewa zai cire tallafin tun a lokacin da yake yakin neman zabe, amma kuma abin ya zo da ba-zata. Kasancewar man fetur ya shafi kusan dukkan bangarorin rayuwar al’umma, nan take aka fuskanci tsadar rayuwa tun daga farashin sufuri da hauhawar farashin kayan masarufi, wanda hakan ya jefa al’ummar Nijeriya cikin halin ni-‘yasu.

  • Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin ‘Yan Ta’adda A Filato
  • Boss Mustapha Ya Karyata Zargin Satar Dala Miliyan 6.3 Daga CBN

Lokacin da Tinubu ya sanar da cire tallafin gaba daya, dokar alkinta albarkatun man fetur ta (PIA) ta riga ta cire tallafin kusan wata 15 da suka gabata amma gwamnatin Shugaba Buhari ta san dabarar da ta shigar da Naira Tiriliyan 3.36 cikin kasafin kudin shekarar 2022 don ta tsawaita lamarin tallafin zuwa watan Yuni na shekarar 2023.

Kungiyar kwadago ta kasa NLC ta bayyana rashin jin dadinta da janye tallafin man, inda ta yi korafin cewa ya kamata gwamnati ta fadada tattaunawa da masu ruwa da tsaki tare da fito da tsare-tsaren da za su rage wa al’umma radadin da janye tallafin zai haifar a rayuwar yau da kullum, ta kuma yi barazanar tsuduma yajin aiki in har gwamnati ba ta yi abin da ya kamata ba. Amma tattaunawar da bangaren gwamnati da shugabannin kungiyar suka yi ta haifar da fahimtar juna duk kuwa da wata kotun tarayya ta haramta wa kungiyar kwadagon shiga yajin aikin, kungiyar kwadagon ta janye yajin aikin da ta shirya shiga ranar Laraba 6 ga watan Yuni.

Don fahimtar halin da al’umma suka shiga sakamakon cire tallafin wani mai sharhi a kan al’amurran yau da kullum, Malam Bashir Dalhatu ya yi nazari da bibiyar rayuwar ‘yan uwa da abokan arziki, inda ya yi nazari halin da magidanci mai ‘ya’ya biyu ke ciki sakamakon cire tallafin man a Nijeriya.

Ya ba da misali da kudin da magidancin zai iya kashewa a abincin rana daya kamar haka: abincin safe, burodi =N600, kosai =N300, ruwan shayi ba madara= N200, ya kama= N1,100, a wata N1,100 sau 30 = N33,000. In kuma in zai yi wainar fulawa, ga yadda za ta kasance, fulawa= N400, Mai N250, Magi N100, kayan miya N50, koko N200, sukari N150, gawayi N100, ya kama: N1,250, kenan a wata, abin da za a kashe ya kama N1,250 sau 30 = N37,500 a cin abin safe kwai.

Abinci rana kuma an kiyasta zai kashe N29,100 a duk wata a abincin dare kuma zai iya kashe N21,900, in aka hada da kudin ruwan sha na N4500 duk wata zai kashe N88,500 kenan a duk wata idan zai sha shayi ba madara kuma ba zai ci abinci da kifi ko nama ba. Idan kuma wainar fulawa zai yi da safe zai kashe N93,000 a wata shi ma dai ban da kifi da nama.

Wannan lissafin na magidanci ne mai ‘ya’ya biyu kuma ba a saka kudin haya, kudin wuta, rashin lafiya, kudin zuwa aiki, omo, sabulu da sauran su.

Idan aka lura da mafi karancin albashi na N30,000 ga ma’aikatan Nijeriya wanda ma har zuwa yanzu wasu jihohi da kananan hukumomi ba su fara aiwatar da biyan albashin ba, tabbas magidanta a Nijeriya sun shiga halin matsi sosai.

Haka kuma ba a hada da kudin makarantar boko na yara, da kudin makarantar islamiyya da na kayan sawa ba wanda dukkan su cire tallafin mai ya shafe su.

2023
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi

Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.