• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Twitter Space Na LEADERSHIP Hausa: Gaskiya Ta Bayyana Kan Bullar Mata Masu Shan Jini

Mun wallafa a ranar 8 ga Satumba, 2023

by Rabi'u Ali Indabawa and Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
in Rahotonni
0
Shirin Twitter Space Na LEADERSHIP Hausa: Gaskiya Ta Bayyana Kan Bullar Mata Masu Shan Jini
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun daga karshen watan Agusta aka rika yada jita-jitar bayyanar wasu mata da suke shiga gidajen mutane wadanda ake musu lakabi da ‘masu shan jini’ a wasu sassa na Arewa musamman Jihar Kano.

An ce wadannan mutane suna yawo ne gida-gida a lokacin da ska tabbatar da mazaje ba sa gida, inda da zarar sun shiga, abin da suke fara nema shi ne a taimaka musu da ruwan sha ko wani abu, wanda kuma da an taimaka musu da abin da suka bukata, to wacce ta ba da taimakon sai a ga ta yanke jiki ta fadi, daga nan lamarin ya kai ga ta rasa ranta.

  • Harin Filato: Gwamnati Ba Za Ta Huta Ba Har Sai An Hukunta Maharan – Shettima 
  • Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

Masu yada maganganun sun ce irin wannan ibtila’i ya faru a unguwanni daban-daban a cikin Birnin Kano.

A wasu bidiyo da suke yawo a kafofin sadarwa na zamani ana ganin yadda ake dukan wadannan mata yayin da aka kama su, sannan kuma a lokacin da ake yi musu tambayoyi sukan kasa ba da wata gamsasshiyar amsa da za ta fahimtar da mutane yadda gaskiyar lamarin yake.

An samu irin wannan lamarin a unguwannin Hotoro, Zango, Rijiyar Lemo, Gwagwarwa, Kwana Hudu Medile, da sauran wasu unguwanni da ke cikin birnin Kano.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Baya ga haka, akwai wani bidiyo da yake yawo na wasu mata ‘yan kauye da aka nuna wasu matasa na yi musu tambayoyi, amma su kuma maganarsu ba irin ta ‘yan Jihar Kano ba ce mutanen Sakkwato ne.

Sannan akwai wani bidiyo na wata baiwar Allah da lamarin ya shafi ‘yarta wacce ‘yar ba ta kai shekara guda da haihuwa ba, inda uwar take bayanin yadda ta rasa ‘yarta ta irin wannan hanya.

Kamar yadda LEADERSHIP Hausa ta bi diddigi, tun da farko daga yankin Kankara da ke Jihar Katsina aka fara samun bullar irin wannan labari, inda aka ce wata tsohuwa ta shiga wani gida inda ta bukaci a taimaka mata da ruwa ta shiga ban daki, shigarta ke da wuya sai matar gidan ta fadi. A cewar labarin sai jini ya fara kwarara daga jikin matar, daga nan sai ita bakuwar ta kama hanyar ficewa daga gidan a kan hanyar fita suka ci karo da mijin matar, tun da bai san abin da ke faruwa ba sai ya bar ta  ta wuce, yana shiga gida sai ya tarar da matarsa cikin jini, hakan tasa ya dawo da gudu, ya nemi gudunmawar al’umma aka kama matar. Bayan yi mata tambayoyi sai ta bayyana cewa su 100 aka turo Jihar Katsina, yanzu haka an kashe tara daga cikinsu, ita ce ta goma. In ji majiyarmu.

Sakamakon yadda lamarin ya yi kamari a tsakanin al’umma, LEADERSHIP Hausa ta gudanar da Shirin Tattaunawa ta Manhajar Twitter Space, inda ta gayyato mai magana da yawun ‘yansanda, reshen Jihar Kano, SP Haruna Abdullahi Kiyawa da kwararriyar mai horarwa da warware mishkilar zamantakewa, shugabar Cibiyar Nurul Huda, Hajiya Fatima Bamalli domin warware zare da abawa kan wannan al’amari.

A jawabin da ya yi, SP Haruna ya tabbatar da wannan jita-jita da ake yadawa inda ya ce tuni rundunarsu ta kaddamar da bincike, yana mai cewa, “Mun samu rahotanni 14 cikin kwana 5 na rufar wa mata da zargin ‘yan shan jini ne, kamar a unguwar Hotoro an samu guda uku, Zango 4,” in ji shi.

“Duk mun gudanar da bincike daya bayan daya, duk binciken da muka yi ba mu samu ko daya a cikin matan da ake zargi da laifin shan jini ba, abu ne na Allah wadai. A Unguwar Kwana 4, wasu ‘yan mata ne suka kai caji a wani gida, kawai daya ta ce wa matar gidan za ta je bandaki sai matar ta kwarma ihu wai budurwar ‘yar shan jini ce, shi kuma maigida da ya zo maimakon ya yi amfani da hankali kawai sai ya kulle ‘yan matan a daki,’yan unguwa suka taru, matar gidan ta daki wadda take zargin, ‘yansanda ne suka kubutar da su.

A nata bangaren, Shugabar Cibiyar Horarwa ta Nurul Huda, Hajiya Fatima Bamalli Bamalli ta yi bayanin cewa,

“Ana ta yadawa muna ganin bidiyos, ana ce wa mutane a daina ba da taimakon ruwan sha kuma a daina bude kofar gida. Gaskiya kowane Dan’adam akwai yakininsa. Da aka fara yadawa, na ce wannan tsafi ne amma ni ban yarda da shi ba. Na daya dai, mu mata daga mahangar addini, Allah ya umarci Manzon Allah ya fada wa muminai a killace mata a gida. Kuma haka nan mata a yanzu ana business ana aiki amma ya kamata a yi bisa sharuddan addini. Abin da ya sa abin ya fi faruwa da mata saboda mu ne muke da sakaci, Wasu make-up da ake yi mara ma’ana, to mai yin irin wannan ne ma abin zai iya kamata. Sannan an manta da yin azkar da addu’o’i shi ya sa ma idan an yi abin zai kama mutum.

“Ni dai ban yarda da abin ba dama. Ba na jin akwai wanda zai zo ya ce na ba shi ruwa na hana shi. Idan ka ciyar ko ka shayar Allah zai ba ka lada. To don me za a hana mutane yi? Ni da nake son yin taimakon saboda Allah ba na tunanin wani abu zai faru in ba alheri ba. Ya kamata mu koma wa wayewar addinin musulunci ba na bature ba kawai. Idan kuma kina azkar wani abu ya faru to ka sani wannan jarrabawa ce kawai. Kuma Allah na iya sa haka ta zama kaffara.” In ji ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rawar Da Kasar Sin Ta Taka A Duniya

Next Post

Xi Jinping Ya Yi Jawabi A Taron Sabuwar Shekara Ta 2024 Na Majalisar CPPCC

Related

Jini
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

2 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 day ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 week ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 week ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Jawabi A Taron Sabuwar Shekara Ta 2024 Na Majalisar CPPCC

Xi Jinping Ya Yi Jawabi A Taron Sabuwar Shekara Ta 2024 Na Majalisar CPPCC

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Jini

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.