• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Ci Gaba Da Alhinin Rasuwar Ghali Na’Aabba

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Ana Ci Gaba Da Alhinin Rasuwar Ghali Na’Aabba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar Nijeriya daga sassa daban-daban na ci gaba da alhinin rasuwar tsohon shugaban majalisar wakilai, Hon. Ghali Umar Na’Abba wanda ya riga mu gidan gaskiya a tsakiyar makon nan.

An gudanar da jana’izarsa a Jihar Kano kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

  • Dalilai 20 Da Ke Sa Dalibai Faduwa Jarrabawa (1)
  • Majalisar NPC Za Ta Fara Zaman Taron Shekara-shekara A Ranar 5 Ga Watan Maris

Na’Abba ya kasance shi ne shugaban majalisar wakilai na hudu, ya rasu yana da shekaru 65 a duniya bayan ya yi fama da rashin lafiya. Tsohon shugaban majalisar ya kasance dan asalin Jihar Kano wanda aka zabe shi a matsayin dan majalisa mai wakiltar Kano ta tsakiya daga 1999 zuwa 2003.

Ya zama shugaban majalisar ne ‘yan watanni bayan kaddamar da majalisar ta hudu biyo bayan murabus din shugaban majalisar na wancan lokaci, Salisu Buhari daga Jihar Kano, kan badakalar jabun takardun makaranta.

Ya taka muhimmiyar rawar a lokacin da ya zama shugaban majalisar wakilai wajen tabbatar da ‘yancin majalisar a tsakanin bangaren gwamnati, wanda hakan ya haddasa rikici tsakaninsa da tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Duk da kasancewarsu ‘ya’yan jam’iyya daya tsakanin Na’Abba da Obasanjo, amma bai hana shi yin gwagwarmaya ba wajen tabbatar da ‘yancin majalisa. Ana ganin cewa rikicinsa da Obasanjo ne ya hana shi ya sake dawowa zauren majalisa.

Kwanan nan ya sauya sheka daga jam’iyyar APC, ya koma babbar jam’iyyar adawa ta PDP.

Tarihinsa ya nuna cewa ya halarci Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya a Jihar Kaduna, inda ya karanta kimiyyar siyasa, kuma ya kammala a shekarar 1979.

Kafin rasuwarsa, Na’Abba ya yi fama da rashin lafiya mai tsanani har sai da ta kai an fitar da shi kasar waje domin nema lafiyarsa, kuma ya dawo Nijeriya bayan ya murmure daga cutar da ba a bayyana ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kyakkyawar Dabi’ar Gawuna Ke Kara Wa Kanawa Aminta Da Nagartarsa -Ibrahim Mabo

Next Post

MDD Ta Yi Maganar Rayuka 190 Da Aka Kashe A Filato

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

1 hour ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

3 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

8 hours ago
Ghali
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 hours ago
Next Post
MDD Ta Yi Maganar Rayuka 190 Da Aka Kashe A Filato

MDD Ta Yi Maganar Rayuka 190 Da Aka Kashe A Filato

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.