• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ceto Matafiya 21 A Kogi Sa’o’i 48 Bayan Sace Su

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
An Ceto Mutum 3 Bayan Musayar Wuta Da ‘Yan Bindiga A Jihar Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an tsaro a Jihar Kogi sun ceto mutane 21 da aka yi garkuwa da su, sa’o’i 48 bayan sace su a ranar a hanyar Ajaokuta zuwa Itobe a jihar.

Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, wanda ya yaba da kokarin jami’an tsaron, ya jaddada cewa ba za’a iya ci gaba da jure aikata miyagun laifuka a jihar ba, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Nijeriya ya ruwaito.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Rufe Kasuwannin Shanu 11 Saboda Matsalar ‘Yan Bindiga A Jihar
  • Tsohuwar Ministar Jin Kai, Sadiya Ba Ta Ƙi Amsa Gayyatarmu Ba – EFCC

Wata sanarwa da mai taimaka wa gwamnan kan harkokin yada labarai, Onogwu Muhammed ya fitar, ta ce tawagar hadin gwiwa ta jami’an tsaro da suka hada da ‘yan sandan Nijeriya, jami’an tsaron farin kaya da ‘yan banga na yankin ne suka yi nasarar ceton.

Wadanda abin ya shafa, galibi matafiya ne, aka shiga da su wani dajin da ba a san ko ina ba a cikin dajin da ke kusa da Karamar Hukumar Ajaokuta ta Jihar Kogi.

Amma Bello da ya samu rahoton faruwar lamarin, ya ba da umarni ga jami’an tsaro da ’yan banga da su gaggauta daukar matakin kubutar da wadanda aka yi garkuwar da su tare da kamo wadanda suka aikata wannan aika-aika.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

“Wannan karbar umarni da suka yi ya nuna jajircewar Bello wajen tabbatar da tsaro da walwalar ‘yan kasa/mazaunan da ke karkashinsa.

“Kokarin jami’an tsaron hadin gwiwar ya samar da sakamako cikin mai kyau sa’o’i 48, wanda ya kai ga nasarar ceto mutaum 21 da aka kama.

“Bugu da kari, aikin ya kai ga cafke wasu daga cikin masu garkuwa da mutane yayin da ake ci gaba da gano wadanda ke hannunsu,” in ji sanarwar.

Bello, wanda ya yaba wa jami’an tsaro bisa gaggauwa da daukar matakan da suka dace, ya kuma jaddada muhimmancin wanzar da zaman lafiya da tsaro a Jihar Kogi.

“Wannan gwamnatin ta himmatu wajen ganin ta bar wata hanya da za ta bi wajen ganin Jihar Kogi ta kasance daya daga cikin jihohin kasar nan mafi aminci.

“Ya yi amfani da damar da ya samu wajen yin gargadi ga masu mugun nufi, ya kuma gargadi masu aikata laifuka kan yin hijira zuwa Kogi domin aikata miyagun laifuka.

“Wannan ya faru ne saboda Kogi wuri ne da ba za a iya shiga a aikata kowane irin laifi ba, don haka wannan gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaron jihar.

“Nasarar da aka yi ta wannan ceto ta zo ne a matsayin shaida ga hadin kai da yunkurin da jami’an tsaro ke yi a Jihar Kogi a karkashin jagorancin Bello,” in ji ta.

Ya kara da cewa sadaukar da kai na kare lafiyar ‘yan kasa, tare da tsayuwar daka wajen yaki da masu aikata laifuka, ya nuna irin sadaukarwar da gwamnati ta yi wajen samar da yanayin da mazauna yankin za su iya rayuwa ba tare da tsoro ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Masu GarkuwaSokotoYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ayyukan Gina Cibiyoyin Masan’antu Da Gina Asibitin A Kauran Namoda

Next Post

“Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023”

Related

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

10 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

13 hours ago
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

17 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

19 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

19 hours ago
Next Post
“Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023”

"Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023"

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.