ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ceto Matafiya 21 A Kogi Sa’o’i 48 Bayan Sace Su

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Kogi

Jami’an tsaro a Jihar Kogi sun ceto mutane 21 da aka yi garkuwa da su, sa’o’i 48 bayan sace su a ranar a hanyar Ajaokuta zuwa Itobe a jihar.

Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, wanda ya yaba da kokarin jami’an tsaron, ya jaddada cewa ba za’a iya ci gaba da jure aikata miyagun laifuka a jihar ba, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Nijeriya ya ruwaito.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Rufe Kasuwannin Shanu 11 Saboda Matsalar ‘Yan Bindiga A Jihar
  • Tsohuwar Ministar Jin Kai, Sadiya Ba Ta Ƙi Amsa Gayyatarmu Ba – EFCC

Wata sanarwa da mai taimaka wa gwamnan kan harkokin yada labarai, Onogwu Muhammed ya fitar, ta ce tawagar hadin gwiwa ta jami’an tsaro da suka hada da ‘yan sandan Nijeriya, jami’an tsaron farin kaya da ‘yan banga na yankin ne suka yi nasarar ceton.

ADVERTISEMENT

Wadanda abin ya shafa, galibi matafiya ne, aka shiga da su wani dajin da ba a san ko ina ba a cikin dajin da ke kusa da Karamar Hukumar Ajaokuta ta Jihar Kogi.

Amma Bello da ya samu rahoton faruwar lamarin, ya ba da umarni ga jami’an tsaro da ’yan banga da su gaggauta daukar matakin kubutar da wadanda aka yi garkuwar da su tare da kamo wadanda suka aikata wannan aika-aika.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

“Wannan karbar umarni da suka yi ya nuna jajircewar Bello wajen tabbatar da tsaro da walwalar ‘yan kasa/mazaunan da ke karkashinsa.

“Kokarin jami’an tsaron hadin gwiwar ya samar da sakamako cikin mai kyau sa’o’i 48, wanda ya kai ga nasarar ceto mutaum 21 da aka kama.

“Bugu da kari, aikin ya kai ga cafke wasu daga cikin masu garkuwa da mutane yayin da ake ci gaba da gano wadanda ke hannunsu,” in ji sanarwar.

Bello, wanda ya yaba wa jami’an tsaro bisa gaggauwa da daukar matakan da suka dace, ya kuma jaddada muhimmancin wanzar da zaman lafiya da tsaro a Jihar Kogi.

“Wannan gwamnatin ta himmatu wajen ganin ta bar wata hanya da za ta bi wajen ganin Jihar Kogi ta kasance daya daga cikin jihohin kasar nan mafi aminci.

“Ya yi amfani da damar da ya samu wajen yin gargadi ga masu mugun nufi, ya kuma gargadi masu aikata laifuka kan yin hijira zuwa Kogi domin aikata miyagun laifuka.

“Wannan ya faru ne saboda Kogi wuri ne da ba za a iya shiga a aikata kowane irin laifi ba, don haka wannan gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaron jihar.

“Nasarar da aka yi ta wannan ceto ta zo ne a matsayin shaida ga hadin kai da yunkurin da jami’an tsaro ke yi a Jihar Kogi a karkashin jagorancin Bello,” in ji ta.

Ya kara da cewa sadaukar da kai na kare lafiyar ‘yan kasa, tare da tsayuwar daka wajen yaki da masu aikata laifuka, ya nuna irin sadaukarwar da gwamnati ta yi wajen samar da yanayin da mazauna yankin za su iya rayuwa ba tare da tsoro ba.

Kogi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
“Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023”

"Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023"

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.