• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ayyukan Gina Cibiyoyin Masan’antu Da Gina Asibitin A Kauran Namoda

by Hussein Yero
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ayyukan Gina Cibiyoyin Masan’antu Da Gina Asibitin A Kauran Namoda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya kaddamar da ayyukan gina cibiya koyon sana’oi uku a Karamar Hukumar Kauran Namoda.

Babban mataimaki na musamman na gwamna Dauda Lawal ne, Suleman Bala Idris, ya bayyana haka a takardar da ya sanya wa hannun ga manema labarai.

  • Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 4 Na Binciken Yanayi Samfurin Tianmu-1
  • Bashin Amurka Ya Kai Sabon Matsayi Wanda Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasar

A cewarsa, an shirya gina cibiyoyin koyar da sana’o’i guda uku a shiyyoyin Sanatoci uku na Jihar Zamfara.

Wadannan cibiyoyi za su kasance kamar haka a karamar hukumar Gusau na shiyyar Zamfara ta Tsakiya, da karamar hukumar Kauran Namoda ta Arewa, da kuma karamar hukumar Gummi ta shiyyar Zamfara ta Yamma.

Ya ce: “A jiya Gwamna Dauda Lawal ya dauki wani muhimmin mataki na cika alkawuran yakin neman zabe ta hanyar kaddamar da muhimman ayyukan more rayuwa a karamar hukumar Kauran Namoda.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

“Gwamnan ya kaddamar da sana’o’i da cibiyar koyar da sana’o’i a Kwalejin Fasaha ta Gwamnati da ke Kauran Namoda. Cibiyar tana da ajujuwa shida, dakin gwaje-gwaje, bita biyu, dakin kwamfuta da ofisoshin ma’aikata.

“A yayin kaddamar da aikin, Gwamna Lawal ya jaddada cewa ilimi na daga cikin manyan abubuwan da gwamnatin Zamfara ta sa gaba, kuma masu ruwa da tsaki suna aiki tare domin ganin an yi wa tsarin karatun jihar garambawul.”

Sauran ayyukan da Gwamna Dauda Lawal ya kaddamar a karamar hukumar sun hada da gina cibiyar ci gaban mata, da makarantun tsangaya, da kuma sake gina babban asibitin Kauran Namoda da gyara shi.

“Cibiyar ci gaban mata za ta kasance cibiyar karfafa mata a mazabar majalisar dattawa. Cibiyar za ta kasance da kayan aiki na zamani don cikakken aiki.

“Gwamna Dauda Lawal ya aza harsashin ginin babban asibitin Kauran Namoda da kuma gyara shi. Ya yi alkawarin samar da kwararrun likitoci da ma’aikatan jinya tare da jaddada kudirinsa na samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya a fadin jihar.

“Kwamitin makarantar Islamiyya ta Tsangaya, Gwamna Dauda Lawal ya sanar da cewa gwamnatin Jihar Zamfara za ta gina irin wadannan makarantu a dukkanin shiyyoyin Sanatoci uku na jihar. Wannan shiri na da nufin sabunta tsarin makarantar Islamiyya ta Tsangaya da samar da damammaki ga daliban”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 4 Na Binciken Yanayi Samfurin Tianmu-1

Next Post

An Ceto Matafiya 21 A Kogi Sa’o’i 48 Bayan Sace Su

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

11 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

12 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

13 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

17 hours ago
Zamfara
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

18 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

19 hours ago
Next Post
An Ceto Mutum 3 Bayan Musayar Wuta Da ‘Yan Bindiga A Jihar Kwara

An Ceto Matafiya 21 A Kogi Sa'o'i 48 Bayan Sace Su

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.