• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fataucin Yara: ‘Yansanda Sun Ceto Jarirai 3, Sun Cafke Mutane 16 A Gombe

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Gombe ta ceto jarirai uku tare da cafke wasu mutane 16 da ake zargi da laifin safarar yara a jihar.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, ASP Mahid Abubakar, ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a madadin kwamishinan ‘yansandan jihar, Hayatu Usman a Gombe a ranar Laraba.

  • CBN Ya Nada Sabbin Shugabannin Gudanarwar Wasu Bankuna
  • Bangaren Layin Dogo Na Sin Ya Yi Jigilar Fasinjoji Mafi Yawa A 2023

Abubakar, ya ce an shigar karar ne a karshen mako biyo bayan rahoton sirri da aka samu daga mutanen yankin Barunde na Jihar Gombe.

Ya ce an ceto jarirai uku daga hannun wadanda ake zargin, yayin da wasu biyu kuma aka yi safarar su daga jihar.

A cewarsa, daya daga cikin jariran da aka yi safarar su a yanzu yana Legas, yayin da dayan kuma an ceto shi a Anambra.

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Ya bayyana cewa ana kokarin kwato sauran jariran biyu da kuma mayar da su jihar.

Abubakar, ya bayyana cewa, yayin bincike, an gano cewa an sayar da daya daga cikin jariran kan Naira 400,000.

Ya ce an sayar da jaririn ga wani mutum a jihar tare da hadin gwiwar wani ma’aikaci a jihar.

A cewar kakakin rundunar ‘yansandan, rundunar ta samu rahoton sirri kan daya daga cikin iyayen da suka sayar da dansu ga wadanda ake zargin.

“Wannan wani laifi ne na hada baki da fataucin yara inda aka kama wata Khadija Manzo da wasu 15 bayan rahoton sirri da aka samu daga al’ummar Barundde a karshen mako.

“A wani lokaci a shekarar da ta gabata, wata Khadija Manzo da wasu 15 sun shiga harkar sayar da jarirai.

“Da samun rahoton, jami’an tsaro na Lowcost Division sun gudanar da bincike wanda ya kai ga kama Manzo, da sauran wadanda ake zargi,” in ji shi.

Abubakar ya ce bincike ya nuna cewa Manzo ya sayar da jarirai biyu ga Ukamaka Ugwu a lokuta daban-daban.

Ya ce an kama wasu da ake zargi da hannu wajen aikata laifin.

Da yake karin bayani, Abubakar ya ce: “Bincike ya nuna cewa ta sayar da wani jariri kan Naira 400,000 ga wata Tina Raphael.

“Kuma ta bayar da Naira 200,000 ga wani Haruna Abubakar, wanda ke aiki da gwamnatin Gombe.

“Yahaya Suleiman ya karbi Naira 200,000 daga hannun ta ya bai wa Haruna Abubakar.

“Ukamaka Ugwu ya sayi yara biyu daya a halin yanzu yana Legas daya kuma a Anambra, amma ‘yansanda na kokarin ganin an dawo da jariran.”

Abubakar ya ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaGombeJariraiSafarar Yara
ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Ya Nada Sabbin Shugabannin Gudanarwar Wasu Bankuna

Next Post

Ogun: Kotun Koli Ta Dakatar Da Karar Korar Abiodun

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

11 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

13 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

16 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

17 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

17 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

18 hours ago
Next Post
Ogun: Kotun Koli Ta Dakatar Da Karar Korar Abiodun

Ogun: Kotun Koli Ta Dakatar Da Karar Korar Abiodun

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.