• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fataucin Yara: ‘Yansanda Sun Ceto Jarirai 3, Sun Cafke Mutane 16 A Gombe

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Gombe ta ceto jarirai uku tare da cafke wasu mutane 16 da ake zargi da laifin safarar yara a jihar.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, ASP Mahid Abubakar, ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a madadin kwamishinan ‘yansandan jihar, Hayatu Usman a Gombe a ranar Laraba.

  • CBN Ya Nada Sabbin Shugabannin Gudanarwar Wasu Bankuna
  • Bangaren Layin Dogo Na Sin Ya Yi Jigilar Fasinjoji Mafi Yawa A 2023

Abubakar, ya ce an shigar karar ne a karshen mako biyo bayan rahoton sirri da aka samu daga mutanen yankin Barunde na Jihar Gombe.

Ya ce an ceto jarirai uku daga hannun wadanda ake zargin, yayin da wasu biyu kuma aka yi safarar su daga jihar.

A cewarsa, daya daga cikin jariran da aka yi safarar su a yanzu yana Legas, yayin da dayan kuma an ceto shi a Anambra.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Ya bayyana cewa ana kokarin kwato sauran jariran biyu da kuma mayar da su jihar.

Abubakar, ya bayyana cewa, yayin bincike, an gano cewa an sayar da daya daga cikin jariran kan Naira 400,000.

Ya ce an sayar da jaririn ga wani mutum a jihar tare da hadin gwiwar wani ma’aikaci a jihar.

A cewar kakakin rundunar ‘yansandan, rundunar ta samu rahoton sirri kan daya daga cikin iyayen da suka sayar da dansu ga wadanda ake zargin.

“Wannan wani laifi ne na hada baki da fataucin yara inda aka kama wata Khadija Manzo da wasu 15 bayan rahoton sirri da aka samu daga al’ummar Barundde a karshen mako.

“A wani lokaci a shekarar da ta gabata, wata Khadija Manzo da wasu 15 sun shiga harkar sayar da jarirai.

“Da samun rahoton, jami’an tsaro na Lowcost Division sun gudanar da bincike wanda ya kai ga kama Manzo, da sauran wadanda ake zargi,” in ji shi.

Abubakar ya ce bincike ya nuna cewa Manzo ya sayar da jarirai biyu ga Ukamaka Ugwu a lokuta daban-daban.

Ya ce an kama wasu da ake zargi da hannu wajen aikata laifin.

Da yake karin bayani, Abubakar ya ce: “Bincike ya nuna cewa ta sayar da wani jariri kan Naira 400,000 ga wata Tina Raphael.

“Kuma ta bayar da Naira 200,000 ga wani Haruna Abubakar, wanda ke aiki da gwamnatin Gombe.

“Yahaya Suleiman ya karbi Naira 200,000 daga hannun ta ya bai wa Haruna Abubakar.

“Ukamaka Ugwu ya sayi yara biyu daya a halin yanzu yana Legas daya kuma a Anambra, amma ‘yansanda na kokarin ganin an dawo da jariran.”

Abubakar ya ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaGombeJariraiSafarar Yara
ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Ya Nada Sabbin Shugabannin Gudanarwar Wasu Bankuna

Next Post

Ogun: Kotun Koli Ta Dakatar Da Karar Korar Abiodun

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

7 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

16 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

18 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

19 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

1 day ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Ogun: Kotun Koli Ta Dakatar Da Karar Korar Abiodun

Ogun: Kotun Koli Ta Dakatar Da Karar Korar Abiodun

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.