• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Da NITDA Sun Kulla Alakar Aiki Don Yaki Da Rashawa Ta Hanyar Fasaha

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
ICPC Da NITDA Sun Kulla Alakar Aiki Don Yaki Da Rashawa Ta Hanyar Fasaha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar yaki da rashawa da dangoginta (ICPC) na jagorantar hadin guiwa da hukumar bunkasa fasahar sadarwa ta kasa (NITDA) wajen yin amfani da fasahar zamani domin dakilewa da toshe kafofin rashawa da babakere da dukiyar al’umma a Nijeriya.

Shugaban ICPC, Musa Aliyu, SAN, a yayin zaman domin kulla kyakkyawar alakar aiki da NITDA da ya gudana a cikin makon jiya, ya ce, babu makawa, rungumar dabarun amfani da hanyoyin fasaha na zamani za su taimaka sosai wajen rage kaifin rashawa a kasar nan.

  • Zargin Badaƙala: Sadiya Ta Kai Kanta Ofishin EFCC
  • Kotu Ta Dakatar Da EFCC, ICPC, DSS Daga Tsare Sanata Yari

Ganawar ta kuma kai ga bada daman hada wata kakkarfar kwamiti da zai kara kyautata alaka a tsakanin hukumomin biyu, wanda a cewar masu ruwa da tsakin, wani mataki ne bullo da sabbin dabarun zamani da hikimomi wajen magance illa da barnar rashawa da cin hanci a Nijeriya.

Shafin Kimiyya da fasaha na LEADERSHIP Hausa ya labarto cewa, ita dai wannan alakar an shirya da tsarata ne tun zamanin mulkin tsohon shugaban ICPC, Farfesa Bolaji Owasanoye, a 2021 da nufin taimakawa kokarinsu wajen yaki da rashawa da toshe haramtatun hanyoyin hada-hadar kudade.

A sanarwar manema labarai da kakakin ICPC Azuka Ogugua ya fitar, ya ce, shugaban ICPC na yanzu, Aliyu ya ziyarci NITDA ne domin tsara sabbin dabarun yaki da rashawa, maida hankali wajen amfani da fasaha domin jagorantar nasarorin ayyukan ICPC kan yaki da rashawa da cin hanci.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Aliyu na cewa, “Da dukkanin amfanun kowace bangare, rungumar dabarun fasaha shi ne muhimman matakin yaki da kuma dakile rashawa. Alakarmu da NITDA na da manufar taimakawa ICPC ne wajen tafiya da zamani, inganta gaskiya, rikon amana, dakile kafofin barnata dukiyar jama’a da kuma inganta amincewar jama’a ga masu jagorantarsu ta hanyar rage kaifin rashawa.

“Yaki da rashawa ba tare da amfani da fasaha ba ba zai yiyu ba a wannan lokacin. Babban nauyin da ke kan ICPC sun hada da har da dakile aikata rashawa, bincike, da gurfanawa. Fasaha zai taimaka mana sosai wajen gudanar da wadannan ayyukan da suke gabanmu,” shugaban ICPC ya shaida.

Shi kuma a nasa bangaren, darakta janar na NITDA, Kashifu Abdullahi, ya nuna kwarin guiwarsu na taimaka wa ICPC wajen cimma manufofin kyautata aiki da ta sanya a gaba.

Ya nanata muhimmancin da ke akwai wajen saukaka aiki da kyautata aikin ta hanyar amfani da fasaha, ya ce, za su kara zaunawa su bullo da muhimman hanyoyin da za su taimaka wa hukumar matuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EFCCICPCNITDA
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwamoti La’ori ya Kaddamar Da Dakin Zana Jarabawa A GDSS Gamadio

Next Post

Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023

Related

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Manyan Labarai

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

51 minutes ago
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

9 hours ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

10 hours ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

13 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

15 hours ago
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
Manyan Labarai

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

17 hours ago
Next Post
Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023

Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.