ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamoti La’ori ya Kaddamar Da Dakin Zana Jarabawa A GDSS Gamadio

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Kwamoti

Wannan lokaci ne na murna ga dalibai, iyaye, da al’ummar yankin raya karkara ta gundumar Vulpi a Karamar Hukumar Numan a Jihar Adamawa, yayin da dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Demsa/Numan/Lamurde ya gina musu dakin zana jarabawa.

Da yake gabatar da jawabi a taron, shugaban makarantar GDSS Gamadio, Mista Zacheaus, wanda ya nuna farin cikinsa, ya bayyana yadda daliban ke tafiya kananan hukumomin Lamurde da Demsa makwabciyarsu domin rubuta jarrabawar WAEC da NECO.

  • Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade
  • An Gano Dukiyar Iyalan Masarautar Saudiyya Ta Fi Ta Masu Arzikin Duniya Biyu Yawa

Ya bayyana cewa ko da aka kafa cibiyoyin WAEC da NECO a shekarar 2019, dole ne a dakatar da darusa don barin ajujuwan da za a yi amfani da su har tsawon lokacin zana jarrabawar, saboda matsalar rashin dakin zana jarabawar da za a yi wa dalibai.

ADVERTISEMENT

Shugaban ya kuma yi kira ga dan majalisar da ya kara kaimi, a fannin dakunan gwaje-gwaje na kimiyya da na’ura mai kwakwalwa gami da inganta ajujuwan makarantun domin bai wa dalibai damar karatu mai inganci.

Shi ma da yake jawabi a taron, dan majalisar, Kwamoti La’ori, ya tabbatar wa al’ummar yankin zai ci gaba da jajircewa na ganin sun kai ga morar mulkin dimokuradiyya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Kwamoti dan majalisa ne da ke kyakkyawar niyya don isar da ayyukan more rayuwa ga al’umma a fadin unguwani 30 na mazabarsa, aikin da masu jawabai da dama a taron suka bayyana da cewa “ba a taba ganin dan majalisa kamar sa ba a tarihin mazabarsa da Jihar Adamawa”.

Dan majalisar bai gushe ba sai da ya bayyana aniyarsa ta ci gaba da inganta fannin ilimi da kuma kudurin kawo sauyi a rayuwar al’ummarsa.

A yayin jawabinsa, ya nuna jin dadinsa ga jama’a bisa goyon bayan da suke ba shi a kowane lokaci.

Shugabannin kananan hukumomin Numan da Lamurde da sarakunan gargajiya da shugabannin jam’iyyun siyasa da masu ruwa da tsaki sun gabatar da jawabin fatan alheri, inda suka yaba da salon shugabancin dan majalisar.

Dalibai da daukacin mahalarta taron sun nuna anshuwa da jin dadinsu a cikin jawabai da kasidu da raye-raye da kuma wakokin yabo ga Allah da ya ba su Honorable Kwamoti La’ori, a matsayin wakilinsu.

Kwamoti
Muh'd Shafi'u Saleh
+ postsBio
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Shahararren Malamin Addinin Islama A Adamawa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware Ya Rasu
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
ICPC Da NITDA Sun Kulla Alakar Aiki Don Yaki Da Rashawa Ta Hanyar Fasaha

ICPC Da NITDA Sun Kulla Alakar Aiki Don Yaki Da Rashawa Ta Hanyar Fasaha

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.