• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Yi Tsokaci Kan Yanayin Da Ake Ciki A Shiyyoyi Daban Daban

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ministan Wajen Kasar Sin Ya Yi Tsokaci Kan Yanayin Da Ake Ciki A Shiyyoyi Daban Daban
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Lahadi, ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya yi tsokaci kan yanayin da ake ciki a wasu shiyyoyi daban daban, a wani taron manema labaru da ya gudana a birnin Alkahira na kasar Masar, bayan da ya gana da takwaransa na kasar Masar Sameh Shoukry.

Dangane da rikicin da ake fama da shi a zirin Gaza, ministan na kasar Sin ya ce, rikicin na ta kara tsanani, lamarin da ya haddasa rasa rayukan dimbin fararen hula, da haifar da mummunan tasiri ga karin yankuna makwabta cikin matukar sauri. A cewar jami’in, kasar Sin a ko da yaushe tana goyon bayan ra’ayi mai dauke da adalci, inda take kokarin neman ganin a tsagaita bude wuta, a hadin gwiwarta da kasashen Larabawa, da na Musulmi, don kare fararen hula, da neman samun damar daidaita batun Falasdinu cikin adalci kuma daga tushe tun da wuri.

  • CMG Ta Kammala Bitar Farko Ta Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Bana
  • Ofishin Kula Da Harkokin Taiwan Na Majalisar Gudanarwa Da Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Sun Yi Tsokaci Kan Sakamakon Zabukan Taiwan

Sa’an nan, game da maganar tsaro da ta shafi bahar Maliya, jami’in Sin ya ce, kasar Sin tana damuwa da mai da cikakken hankali kan batun. Kana kasar ta yi kira da a dakatar da kai hari ga jiragen ruwa na fararen hula, don kare tsarin samar da kayayyaki da na cinikayya a duniya. A cewar Malam Wang, dalilin da ya sa ake samun tashin hankali a yankin bahar Maliya, shi ne habakar rikici daga zirin Gaza zuwa sauran wurare. Yanzu aikin da ya kamata a aiwatar da shi cikin gaggawa shi ne, a kwantar da kurar da ta tashi a Gaza, don magance ci gaban bazuwar rikicin.

Ban da haka, jami’in ya yi tsokaci kan yanayin da ake ciki a yankin Taiwan na kasar Sin. Ya ce, zaben da aka yi a yankin, aikin cikin gida ne na kasar Sin. Kana duk wani sakamakon da aka samu wajen zaben, ba zai canza hakikanin yanayin da ake ciki ba, wato kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kana Taiwan wani yanki ne na kasar Sin. Kana ba zai girgiza ra’ayi na bai daya da gamayyar kasa da kasa ke da shi na kasancewar kasar Sin guda daya kawai ba.

Bugu da kari, Mr. Wang Yi wanda yake kai ziyara kasar Tunisia, ya bayyana sabon kwalejin nazarin harkokin diflomasiyyar kasa da kasa na Tunis, wato kwaleji daya tilo na harkokin diflomasiyya da aka kaddamar a yau Litinin, kuma Sin ta taimaka wajen ginawa a wata kasar Larabawa, a matsayin sabuwar alama ta dankon zumunta, kuma dandalin raya abotar Sin da Tunisia.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Wang Yi ya bayyana haka ne yau, lokacin da yake jawabi yayin bikin bude kwalejin a birnin Tunis. Bikin ya samu halartar shugaban kasar, Kais Saied da ministan harkokin wajen kasar, Nabil Ammar.

Wang Yi ya kuma yi kira da a yi kokarin inganta gina tsarin duniya mai daidaito tsakanin kasashen duniya da dama da dunkulewar tattalin arzikin duniya domin kowa ya amfana. (Bello Wang, Fa’iza Mustapha)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasashe Da Dama Na Adawa Da Yunkurin Ware Taiwan Daga Babban Yankin Kasar Sin

Next Post

Muna Bukatar Dala Biliyan 1 Don Ceto Rayuka A 2024 – WHO

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

13 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

14 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

16 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

19 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

20 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

21 hours ago
Next Post
Muna Bukatar Dala Biliyan 1 Don Ceto Rayuka A 2024 – WHO

Muna Bukatar Dala Biliyan 1 Don Ceto Rayuka A 2024 - WHO

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.