ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Yi Tsokaci Kan Yanayin Da Ake Ciki A Shiyyoyi Daban Daban

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A jiya Lahadi, ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya yi tsokaci kan yanayin da ake ciki a wasu shiyyoyi daban daban, a wani taron manema labaru da ya gudana a birnin Alkahira na kasar Masar, bayan da ya gana da takwaransa na kasar Masar Sameh Shoukry.

Dangane da rikicin da ake fama da shi a zirin Gaza, ministan na kasar Sin ya ce, rikicin na ta kara tsanani, lamarin da ya haddasa rasa rayukan dimbin fararen hula, da haifar da mummunan tasiri ga karin yankuna makwabta cikin matukar sauri. A cewar jami’in, kasar Sin a ko da yaushe tana goyon bayan ra’ayi mai dauke da adalci, inda take kokarin neman ganin a tsagaita bude wuta, a hadin gwiwarta da kasashen Larabawa, da na Musulmi, don kare fararen hula, da neman samun damar daidaita batun Falasdinu cikin adalci kuma daga tushe tun da wuri.

  • CMG Ta Kammala Bitar Farko Ta Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Bana
  • Ofishin Kula Da Harkokin Taiwan Na Majalisar Gudanarwa Da Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Sun Yi Tsokaci Kan Sakamakon Zabukan Taiwan

Sa’an nan, game da maganar tsaro da ta shafi bahar Maliya, jami’in Sin ya ce, kasar Sin tana damuwa da mai da cikakken hankali kan batun. Kana kasar ta yi kira da a dakatar da kai hari ga jiragen ruwa na fararen hula, don kare tsarin samar da kayayyaki da na cinikayya a duniya. A cewar Malam Wang, dalilin da ya sa ake samun tashin hankali a yankin bahar Maliya, shi ne habakar rikici daga zirin Gaza zuwa sauran wurare. Yanzu aikin da ya kamata a aiwatar da shi cikin gaggawa shi ne, a kwantar da kurar da ta tashi a Gaza, don magance ci gaban bazuwar rikicin.

ADVERTISEMENT

Ban da haka, jami’in ya yi tsokaci kan yanayin da ake ciki a yankin Taiwan na kasar Sin. Ya ce, zaben da aka yi a yankin, aikin cikin gida ne na kasar Sin. Kana duk wani sakamakon da aka samu wajen zaben, ba zai canza hakikanin yanayin da ake ciki ba, wato kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kana Taiwan wani yanki ne na kasar Sin. Kana ba zai girgiza ra’ayi na bai daya da gamayyar kasa da kasa ke da shi na kasancewar kasar Sin guda daya kawai ba.

Bugu da kari, Mr. Wang Yi wanda yake kai ziyara kasar Tunisia, ya bayyana sabon kwalejin nazarin harkokin diflomasiyyar kasa da kasa na Tunis, wato kwaleji daya tilo na harkokin diflomasiyya da aka kaddamar a yau Litinin, kuma Sin ta taimaka wajen ginawa a wata kasar Larabawa, a matsayin sabuwar alama ta dankon zumunta, kuma dandalin raya abotar Sin da Tunisia.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Wang Yi ya bayyana haka ne yau, lokacin da yake jawabi yayin bikin bude kwalejin a birnin Tunis. Bikin ya samu halartar shugaban kasar, Kais Saied da ministan harkokin wajen kasar, Nabil Ammar.

Wang Yi ya kuma yi kira da a yi kokarin inganta gina tsarin duniya mai daidaito tsakanin kasashen duniya da dama da dunkulewar tattalin arzikin duniya domin kowa ya amfana. (Bello Wang, Fa’iza Mustapha)

 

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Muna Bukatar Dala Biliyan 1 Don Ceto Rayuka A 2024 – WHO

Muna Bukatar Dala Biliyan 1 Don Ceto Rayuka A 2024 - WHO

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.