• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin ‘Yan Bindiga: Jama’a Sun Yi Zanga-zanga A Kaduna, Sun Nemi Taimakon Sarkin Zazzau

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Harin ‘Yan Bindiga: Jama’a Sun Yi Zanga-zanga A Kaduna, Sun Nemi Taimakon Sarkin Zazzau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar kauyen Tunburku da ke unguwar Kidandan a Karamar Hukumar Giwa a Jihar Kaduna, sun gudanar da zanga-zangar lumana don nuna rashin dadinsu kan yadda ‘yan bindiga da suka addabi yankin.

Masu zanga-zangar da suka hada da matasa da tsofaffi, sun yi tattaki zuwa fadar masarautar Zazzau da ke Zariya.

  • Ba Wa Matasa Ilimi Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro – Tinubu
  • Za A Rataye Mutane 2 Sakamakon Kashe Dan Acaba A Adamawa

Malam Yusuf Jibrin, wanda ya yi magana a madadin al’ummar yankin, ya bayyana irin abubuwan da al’ummar ke fuskanta a sakamakon hare-haren ‘yan bindiga.

Ya bayyana yadda hare-haren ‘yan bindiga ke gurgunta ayyukan noma da tattalin arziki, sannan yake haifar da babbar barazana ga zaman lafiya da tsaron daukacin al’ummar yankin.

Malam Amiru Abubakar, wani mazaunin garin, ya bayyana irin ta’asar da ‘yan bindiga ke yi ta hanyar kashe-kashe da sace-sace da kuma karbar haraji ga manoma don neman izinin yin noma.

Labarai Masu Nasaba

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Ya kara bayyana irin yadda mata ke fuskantar cin zarafi fyade da kuma sace-sacen dabbobi, wanda hakan ya sa gidaje da dama ba su da isasshen abinci.

“Suna sace mana dabbobi kuma sun dauke mu kamar bayi,” Abubakar ya koka.

A martaninsa, Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, yayin da yake jajanta wa al’ummar, ya bayyana cewa ya sha samun irin wadannan rahotanni daga yankin.

“A gaskiya lamarin tsaro a Karamar Hukumar Giwa yana hana mu barci,” in ji Bamalli.

Sarkin ya tabbatar wa al’ummar jihar zai jajirce don ganin an magance matsalolinsu.

Ya yi alkawarin mika lamarin ga hukumomin da abin ya shafa domin daukar matakin da ya dace da gaggawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HariKadunaMatsalar TsaroSarkiYan bindigaZariyaZazzau
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Wa Matasa Ilimi Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro – Tinubu

Next Post

Buhari Bai Taba Tsoma Baki A Mulkina Ba – Tinubu

Related

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
Labarai

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

2 hours ago
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

3 hours ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

4 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

14 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

15 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

17 hours ago
Next Post
Buhari Bai Taba Tsoma Baki A Mulkina Ba – Tinubu

Buhari Bai Taba Tsoma Baki A Mulkina Ba - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.