• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Umarci A Sake Cafko Mata Dakta Idris Dutsen Tanshi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Dutsen Tanshi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar Kotun Shari’a da ke Bauchi a ranar Laraba ta warware belin fitaccen malamin addinin Musulunci kuma babban limamin masallacin Juma’a na Dutsen Tanshi da ke Bauchi, Dakta Idris Abdul’aziz tare da umartar a sake kamoshi bisa rashin halartar zaman kotun domin ci gaba da shari’ar tuhumar da ake masa.

Kotun a karkashin mai shari’a Malam Hussaini A. Turaki, ta ki amincewa da bukatar da Lauyan mai kariya ya shigar a gabanta da ke nusar da kotun cewa, sun daukaka kara kan wannan lamarin a kotun daukaka kara da ke Jos don haka ya nemi kada kotun ta cigaba da batu kan shari’ar.

  • Ali Nuhu Da Murja Kunya Na Cikin Mutane 150 Ma Fi Tasiri A Intanet A 2023
  • Harin ‘Yan Bindiga: Jama’a Sun Yi Zanga-zanga A Kaduna, Sun Nemi Taimakon Sarkin Zazzau

Nan take, lauyan gwamnatin jihar ya soki bukatar tare da cewa ba a bi matakan da suka dace na gabatar da wani batun daukaka kara ba.

Sai dai bayan sauraron muhawarar kowani bangare, Mai shari’a ya cimma matsayar cewa, dole ne wanda ake zargi ya bayyana a gaban kotun domin ci gaba da sauraron karar da ake masa.

Idan za a tuna dai, ana zargin babban malamin ne da furta wasu kalamai da ka iya barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali hadi da tunzura jama’a a jihar. Kodayake, a watannin baya malamin har gidan yari ya je amma daga bisani aka samu belinsa.

Labarai Masu Nasaba

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

A ranar Labarar bayan dawowa ci gaba da sauraron karar, lauyan masu shigar da kara, UB Umar na ma’aikatar shari’a ta jihar Bauchi, ya ce, ba kotu ne ko masu shigar da kara za su gabatar da bukata a madadin wanda ake zargi ba, inda ya ce su din sun gaza yin hakan.

Ya ce, “Mun aike masa da sammaci daban-daban, a bayyane balo-balo ya fito ya ce shi ba zai zo kotu ba, muka sake canza sammacin aka manna a addireshinsa domin ba shi damar zuwa kotu.

“Sannan, akwai bukata wacce lauyansa ya shigar, amma ba a gabatar da ita ba.”

Acewar lauyan, kotu ba ta amfani da jita-jita illa abun da aka zo gabanta aka gabatar, don haka, masu kariya ba su bi matakan da suka dace na cewa sun daukaka kara kan shari’ar ba.

“Don haka kotu ta yi umarnin dole ya zo gabanta ya mata bayanin menene dalilinsa na kin halartar zaman da aka yi ta yi a baya, idan yana da hujja mai karfi na yin hakan shi kenan, nan gaba za mu san abun yi.”

Barista UB Umar ya kara da cewa, “Tun da an mika masa sammaci bai zo ba, mataki na gaba shi ne bai wa jami’an tsaron izinin kamoshi gami da gabatar da shi a zaman da kotun za ta yi mako mai zuwa a ranar 24 ga watan nan.”

Shi kuma a bangarensa, lauyan kariya, Ahmad M Umar, ya ce umarnin kamo malamin ba daidai ba ne domin sun sanar da kotun cewa, wannan shari’ar na gaban kotun daukaka kara, don haka, akwai bukatar kotun shari’ar ta mutunta kotun daukaka kara da ke Jos kafin kowane mataki.

Ya ce, “Mun tunatar da koun cewa soke belin wanda ake zargi ba daidai ba ne, sun yi ne bisa kuskure, saboda batun na gaban kotun daukaka kara.

“Mun tunatar da kotun cewa wannan kes din daga wannan kotun zuwa babban kotu sannan zuwa kotun daukaka kara da ke Jos. Mun gabatar da batun ga wannan kotun da sauran bangarorin da lamarin ya shafa tare da notices har guda hudu. Amma sakamakon shari’un zabukan gwamnoni, kotun daukaka karan ba ta samu damar zaunawa kan lamarin ba.

“Yanzu, kotun daukaka ta sake bayar da rana kuma mun shaida wa wannan kotun muka nemi kada ta yi komai domin mutunta matakin kotun daukaka kara, amma duk da suka haka ta soke belin da umarnin a kamo wanda muke karewa.”

Ya ce, matsayarsu shi ne akwai kes din da ke gaban kotun daukaka kara, kuma kotun daukaka kara na gaba da babban kotu balle kotun shari’a. Ya bada tabbacin cewa za su bi matakan da shari’a ta gindaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dutsen TanshiJihar Bauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Bauchi Ta Ceto Rayuka Fiye Da 310 A 2023

Next Post

NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

Related

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi
Manyan Labarai

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

6 hours ago
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna
Manyan Labarai

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

7 hours ago
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya
Labarai

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

9 hours ago
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe
Labarai

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

10 hours ago
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC
Labarai

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

11 hours ago
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara
Manyan Labarai

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

14 hours ago
Next Post
NIS

NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

LABARAI MASU NASABA

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

August 11, 2025
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

August 11, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

August 11, 2025
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

August 11, 2025
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

August 11, 2025
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.