• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: Yadda Abubuwan Mamaki Ke Faruwa A Gasar

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Afcon
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu an kammala wasannin kasashe 16 kuma a yau za a fara wasannin kusa da na kusa da na karshe a wasannin da kasar Ibory Coast take karbar bakunci ta gasar cin kofin nahiyar Afirka karo na 34 a tarihi.

Tuni aka samu kasashe guda takwas da za su fafata a zagayen kusa da na kusa da na karshe a gasar kuma gasar tana ci gaba da baI wa marada kunya tare da ba da mamaki ganin yadda manyan kasashe suke shan kashi a hannun kasashen da ba a yi tsammani ba.

  • AFCON 2023: Masu Masaukin Baƙi Sun Fitar Da Ƙasar Mali
  • Minista Yaɗa Labarai Ya Nemi Masu Zanen Gine-gine Su Farfaɗo Da Tarihin Ginin  Nijeriya

Hakan kuma ya kara wa gasar daraja da girma, sannan kuma hukumomin da suka shirya gasar suna ci gaba da samun jinjina daga masu kallo da masu sharhi a kan kwallon kafa bisa bajintar da suka nuna na ganin gasar da tafi yadda a ka tsara.

Kawo yanzu kasashen da suka kai matakin kusa da na kusa da na karshe sun hada da tawagar Super Eagles ta Nijeriya sai mai masaukin baki Ibory Coast wadda ta doke mai kare kambu wato Senegal, sai kuma kasar Angola wadda itama tana nuna bajinta a wannan gasar.

Kasashen Congo da Guinea ma sun samu damar tsallakawa zuwa mataki na gaba sai kuma kasashen Cape Berde da Afirka ta Kudu da Mali duka sun samu damar tsallakawa zuwa mataki na gaba wanda mataki ne da yake da matukar hatsari.

Labarai Masu Nasaba

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

 

NIJERIYA Da ANGOLA

Tawagar kwallon kafa ta Nijeriya ta kai zagayen dab da na kusa da na karshe, bayan doke Kamaru da ci 2-0 a wasan zagaye na biyu a gasar kofin Afirka kuma tun kafin hutu, Super Eagles ta ci kwallon farko ta hannun Ademola Lookman, sannan kafin nan an soke wadda Semi Ajayi ya fara cin Kamaru wadda aka ce ya yi satar gida.

Bayan da aka yi hutu ne aka koma zagaye na biyu Kamaru ta yi ta kokarin farke kwallon da aka zura mata, amma ba ta samu dama da yawa ba, sannan dab da za a tashi daga wasan ne Super Eagles ta kara ta biyu ta hannun Ademola Lookman, hakan ya sa tawagarta kai zagayen kusada da na kusa da na karshe.

Da wannan sakamakon Nijeriya za ta fafata a zagayen dab da na kusa da na karshe da Angola yau Juma’a 2 ga watan Fabrairu, kuma gabanin fafatawar Nijeriya da Kamarun a ranar Asabar, Angola ta doke Namibia 3-0 a wasan farko a zagaye na biyu na wasannin da ake buga wa a Ibory Coast.

Nijeriya mai kofin Afirka uku jimilla ta yi nasara a kan Kamaru karo na uku a babbar gasar tamaula ta Afirka da suka hadu a baya-bayan nan saboda Super Eagles ta yi nasara a kan Kamaru a zagayen kuarter finals a 2004 da aka yi a Tunisia, sannan Nijeriya ta doke Kamaru 3-2 a wasannin da aka gudanar a Masar a 2019.

Nijeriya ta kawo matakin zagaye na biyu a Ibory Coast, bayan da ta yi ta biyu a rukunin farko da maki bakwai, iri daya da na Ekuatorial Guinea, wadda ta yi ta daya bayan ta yi raga-raga da mai masaukin baki.

Super Eagles ta hada maki bakwai ne, bayan tashi 1-1 da Ekuatorial Guinea a wasan farko a rukuni na daya da cin Ibory Coast 1-0 da kuma nasara a kan Guinea – Bissau 1-0.

Ita kuwa Kamaru ta yi ta biyu ne a rukuni na uku, bayan da ta yi 1-1 da Guinea da rashin nasara 3-1 a hannun Senegal, sannan ta doke Gambia 3-2 kuma Kamaru mai AFCON biyar ta fara da lashe kofin Afirka a kan Nijeriya a 1984 da cin 3-1 da kuma 1988 da ta yi nasarar cin 1-0 da kuma a 2000 da suka tashi 2-2, Kamaru ta lashe kofin a bugun fenariti 4-3 a Nijeriya.

 

CONGO Da GUINEA

Tabbas abin mamaki ne a ce tawagar ‘yan wasan Congo ta iya yin karfin hali ta doke ta Masar a bugun daga kai sai mai tsaron raga bayan sun tashi wasa 1-1 kuma wasa ne wanda za a iya cewa an yi kare jini biri jini wanda sai da ta kai an yi minti 120 ana gwabzawa.

Kasar Masar ita ce wadda tafi kowacce kasa yawan lashe kofin a tarihi domin ita ce ta lashe sau bakwai wanda hakan ya sa ake ganin tana da tarihi mai kyau a gasar wanda kuma yake taimaka mata a duk lokacin da aka zo buga gasar.

Doke kasar Masar da Congo ta yi ya nuna cewa tabbas karfi ya kawo kuma kasar ta Congo, wadda ta yi ta biyu da maki uku a cikin rukunin da ya hada da Morocco da Zambia da kuma Tanzania za ta iya kai wa matakin da ba a yi zato ba a yanzu.

Sai dai itama Guinea ba kanwar lasa bace domin ta uku ta yi a cikin rukunin da ya hada da mai kare kambu Senegal da Kamaru da kuma Gambia kuma ta hada maki hudu ne wanda hakan ya bata damar fitowa daga cikin rukunin.

Sannan bayan fitowarta ta hadu da takwararta ta Ekuatorial Guinea kuma ta doke ta wanda hakan ya sa ake ganin ita ma za ta iya ba da mamaki a wasan da za ta kece raini da Congo, wasa ne wanda za a fafata a filin wasa na Stade Olympikue Alassane Ouattara.

 

MALI Da IBORY COAST

Mali, wadda ta fito daga cikin rukunin da ya hada da Afirka ta Kudu da Namibia da Tunisia ita ce ta yi ta daya a cikin nrukunin kuma tana da matasan ‘yan wasa, sannan kuma kokarin da ta yi ta doke kasar Burkina Faso

Masu masaukin baki Ibory Coast sun shammaci duniya, sun fito a matsayin ‘yan alfarma kuma sun doke kasar Senegal, mai kare kambu, wadda take da manyan ‘yan wasa irinsu Sadio Mane da Khalilou Koulibally da Michael Jackson da sauransu.

Har ila yau, Ibory Coast wadda take karbar bakunci tana da zakakuran ‘yan wasa irinsu Ibrahim Sangare da Frankie Kessie da Fofana da sauransu za ta iya lashe kofin kasancewar ta a gida kuma tana da karfin lashe wasa duk da cewa ta kori kociyanta sakamakon rashin tabuka abin a zo a gani.

 

CAPE BERDE Da AFIRKA Ta Kudu

Kasar Cape Berde, wadda ta ba wa duniya mamaki a wannan gasar ta fito a cikin rukunin da ya hada da manyan kasashe irinsu Ghana, mai kofin Afirka guda biyar, da Masar, wadda ta fi kowacce kasa lashe kofin da guda bakwai sai kuma Mozambikue, kuma haka ta ba wa duniya mamaki.

A wasa na farko Cape Berde ta doke kasar Ghana da ci 2-1 sannan ta doke kasar Mozambikue da ci uku babu ko daya sai kuma suka buga 2-2 da kasar Masar, hakan ya sa ake ganin tabbas Cape Berde za ta ba wa mutane mamaki ko kuma ma ta iya lashe kofin duk da cewa akwai manyan kasashe irinsu Nijeriya da Ibory Coast da sauransu.

Sai dai itama Afirka ta Kudu ba karamin bajinta ta nun aba musamman wajen fitowa daga cikin rukunin da ya hada da Mali da Namibia da Tunisia kuma ta doke tawagar ‘yan wasan kasar Morocco wadda ake ganin babu tawaga mai karfinta a Afirka idan aka kalli bajintar da suka nuna a gasar cin kofin duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Minista Idris Ya Ƙaddamar Da Ƙungiyar Kakakin Labarai 

Next Post

Watakila Rashford Ya Bar Manchester United

Related

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
Wasanni

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

4 hours ago
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan
Wasanni

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

7 hours ago
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal
Wasanni

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

7 hours ago
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

2 days ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

4 days ago
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

5 days ago
Next Post
Watakila Rashford Ya Bar Manchester United

Watakila Rashford Ya Bar Manchester United

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Afcon

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.