ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Watakila Rashford Ya Bar Manchester United

by Sulaiman
2 years ago
Rashford

Kawo yanzu dai dan wasa Marcus Rashford, dan kwallon tawagar Ingila, Marcus Rashford wanda ba ya kan ganiya, yana fuskantar kalubale a Manchester United a kakar bana.

Dan wasan mai shekara 26 ya kasa ci gaba da nuna irin kwazon da ya yi a bara, inda ya ci kwallo 30 a dukkan fafatawa a kungiyar kuma Rashford ya taimaka wa United ta dauki Carabao Cup da samun gurbin Champions League a kakar da ta wuce.

  • Minista Idris Ya Ƙaddamar Da Ƙungiyar Kakakin Labarai 
  • AFCON 2023: Masu Masaukin Baƙi Sun Fitar Da Ƙasar Mali

A kakar wasa ta shekara ta 2023 zuwa 2024, ya ci kwallo hudu a wasanni 26 da ya buga wa Manchester United – kenan kwazonsa ya yi kasa sosai, musamman a Premier League.

ADVERTISEMENT

Saboda haka wasu ke cewa ya kamata Erik ten Hag ya sayar da Rashford ko kungiyar za ta samu kudin sayen wani dan kwallon domin ta kara karfi. To sai dai kuma ba matsalar Rashford kadai United, wadda aka fitar daga Champions League da Carabao Cup da ta dauka a bara ke fustanta ba a kakar nan.

Kungiyar wadda take ta takwas a kan teburin Premier League da maki 32 bayan wasa 21 ta kai zagaye na biyar a FA Cup bayan ta doke kungiyar Newton County a ranar Lahadin da ta gabata.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

A bara ne Rashford ya saka hannu kan yarjejeniyar ci gaba da zama a Manchester United zuwa karshen kakar wasa ta 2028 kan £325,000 a duk mako sannan tun farkon kwantiragin dan kwallon tawagar Ingila zai kare ne a karshen kakar shekara ta 2023 zuwa 2024.

Dan wasan ya taka rawar gani a bara karkashin Erik tten Hag da cin kwallo 30 a wasa 56 a dukkan fafatawa domin ya fara buga wa United wasa a shekarar 2016 a wasa da Midtjylland, kuma kungiyoyi da yawa sun so daukar Rashford a kakar da ta wuce, bayan rawar da ya taka.

Rashford na daya daga cikin ‘yan kwallon Ingila da suka fuskanci kalaman wariya, bayan da ya barar da fenariti a wasan karshe da Italiya a Euro 2020, sannan cikin Agustan shekara ta 2021 ya ji rauni a allon kafada a kakar da ya ci kwallo biyar da ta kai an sallami Ole Gunnar Solskjaer aka maye gurbinsa da Ralf Rangnick.

Bugu da kari, kociyan tawagar Ingila, Gareth Southgate ya ajiye Rashford daga buga wasa hudu a Nations League a cikin watan Yunin shekara ta 2022 sakamakon rashin tabuka abin kirki.

Rashford
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Gwamnonin PDP Sun Goyi Bayan Kiraye-kirayen Kafa ‘Yansandan Jihohi

Zaɓen Cike-gurbi: PDP Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Kujerar Majalisar Tarayya A Jihar Jigawa

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.