ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Watakila Rashford Ya Bar Manchester United

by Sulaiman
2 years ago
Rashford

Kawo yanzu dai dan wasa Marcus Rashford, dan kwallon tawagar Ingila, Marcus Rashford wanda ba ya kan ganiya, yana fuskantar kalubale a Manchester United a kakar bana.

Dan wasan mai shekara 26 ya kasa ci gaba da nuna irin kwazon da ya yi a bara, inda ya ci kwallo 30 a dukkan fafatawa a kungiyar kuma Rashford ya taimaka wa United ta dauki Carabao Cup da samun gurbin Champions League a kakar da ta wuce.

  • Minista Idris Ya Ƙaddamar Da Ƙungiyar Kakakin Labarai 
  • AFCON 2023: Masu Masaukin Baƙi Sun Fitar Da Ƙasar Mali

A kakar wasa ta shekara ta 2023 zuwa 2024, ya ci kwallo hudu a wasanni 26 da ya buga wa Manchester United – kenan kwazonsa ya yi kasa sosai, musamman a Premier League.

ADVERTISEMENT

Saboda haka wasu ke cewa ya kamata Erik ten Hag ya sayar da Rashford ko kungiyar za ta samu kudin sayen wani dan kwallon domin ta kara karfi. To sai dai kuma ba matsalar Rashford kadai United, wadda aka fitar daga Champions League da Carabao Cup da ta dauka a bara ke fustanta ba a kakar nan.

Kungiyar wadda take ta takwas a kan teburin Premier League da maki 32 bayan wasa 21 ta kai zagaye na biyar a FA Cup bayan ta doke kungiyar Newton County a ranar Lahadin da ta gabata.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

A bara ne Rashford ya saka hannu kan yarjejeniyar ci gaba da zama a Manchester United zuwa karshen kakar wasa ta 2028 kan £325,000 a duk mako sannan tun farkon kwantiragin dan kwallon tawagar Ingila zai kare ne a karshen kakar shekara ta 2023 zuwa 2024.

Dan wasan ya taka rawar gani a bara karkashin Erik tten Hag da cin kwallo 30 a wasa 56 a dukkan fafatawa domin ya fara buga wa United wasa a shekarar 2016 a wasa da Midtjylland, kuma kungiyoyi da yawa sun so daukar Rashford a kakar da ta wuce, bayan rawar da ya taka.

Rashford na daya daga cikin ‘yan kwallon Ingila da suka fuskanci kalaman wariya, bayan da ya barar da fenariti a wasan karshe da Italiya a Euro 2020, sannan cikin Agustan shekara ta 2021 ya ji rauni a allon kafada a kakar da ya ci kwallo biyar da ta kai an sallami Ole Gunnar Solskjaer aka maye gurbinsa da Ralf Rangnick.

Bugu da kari, kociyan tawagar Ingila, Gareth Southgate ya ajiye Rashford daga buga wasa hudu a Nations League a cikin watan Yunin shekara ta 2022 sakamakon rashin tabuka abin kirki.

Rashford
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Gwamnonin PDP Sun Goyi Bayan Kiraye-kirayen Kafa ‘Yansandan Jihohi

Zaɓen Cike-gurbi: PDP Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Kujerar Majalisar Tarayya A Jihar Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.