• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Lashe Zabukan Cike Gurbi, Tsohon Kakakin Majalisar Bauchi Ya Dawo Majalisa

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
PDP Ta Lashe Zabukan Cike Gurbi, Tsohon Kakakin Majalisar Bauchi Ya Dawo Majalisa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Kakakin Majalisar dokokin jihar Bauchi, Abubakar Y. Sulaiman, da tsohon mataimakinsa Umaru Dahiru Jamilu (PDP) sun sake komawa Majalisar dokokin jihar biyo bayan nasarar da suka samu a zaben cike gurbi da ya gudana a ranar Asabar. 

Abubakar ya samu nasara ne kan babban abokin karawarsa na jam’iyyar APC, Khalid Abdulmalik.

  • Zaɓen Cike-gurbi: NNPP Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Kujeru Biyu Na Majalisar Jiha A Kano
  • Minista Idris Ya Ƙaddamar Da Ƙungiyar Kakakin Labarai 

Da yake sanar da sakamakon zaben, baturen zaben cike gurbin dan Majalisar Ningi, Farfesa Ahmad Abdulhameed ya ce Abubakar Y Sulaiman na PDP ya samu nasara ne da kuri’u 11,785 yayin da abokin nemansa na APC Khalid ya samu kuri’u 10,339.

Kazalika, a mazabar cikin garin Bauchi, Hon. Umaru Dahiru Jamilu na PDP shi ne ya lashe zaben cike gurbin, inda ya samu nasarar kayar da Kwamared Aliyu Ilale na jam’iyyar APC.

Baturen zaben mazabar Bauchi cikin gari, Farfesa Isma’ila Y Shehu ya ce, Umaru Dahiru Jamilu (PDP) ya lashe zaben ne da kuri’u 45,240 yayin da Abdullahi Aliyu (APC) ya samu kuri’u. 41,266.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

Umaru Dahiru dai shi ne mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi kafin kotun daukaka kara ta soke nasarar da ya samu. Da wannan matakin zai sake komawa majalisa a matsayin mamba.

Haka zancen yake a mazabar wajen garin Bauchi wato Zungur/Galambi inda baturen zaben Farfesa Adamu Samaila na jami’ar ATBU ya shelanta Hon. Yusuf Ahmed na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben mazabar da kuri’u 2,233, hakan ya ba shi nasarar kayar da abokin nemansa Ibrahim Isa Yuguda na jam’iyyar APC da ya tashi da kuri’u 1,928.

Bugu da kari, kujerar dan majalisar Madada/Chinade kuwa, Baturen zaben mazabar, Farfesa Ahmed Abdulkadir ya ayyana Ala Nasiru Ahmed na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’u 13,920 da ya mangare babban abokin nemansa na APC Dantala Ali mai samun kuri’u 9,710.

Jam’iyyar PDP da ke mulki a jihar ta Bauchi ta lashe dukkanin kujerun ‘yan majalisun da aka gudanar a zaben cike gurbi a mazabar Zungur/Galambi, Ningi, da Madara/Chinade.

Sake zaben na zuwa ne bayan da kotun daukaka kara ta soke nasarar da ‘yan majalisun hudu suka samu a zaben ranar 18 ga watan Maris na 2023. Bayan hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben mazabun, kotun daukaka kara ta umarci INEC ta sake gudanar da zabe a rumfuna 42 da suke gundumomin zabe 16 a cikin kananan hukumomi uku na Ningi, Bauchi da Katagum bayan kalubalantar nasarar su da abokan hamayyarsu suka yi.

Sai dai bayan saken zaben dukkanin wadanda aka yi jayayya a kan kujerun su sun sake dawowa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukuncin Kotun kolisiyasar NijeriyaZabukan cike gurbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

Next Post

Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

2 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

4 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

6 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

8 hours ago
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Labarai

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

9 hours ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

10 hours ago
Next Post
Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Bauchi

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.