ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Lashe Zabukan Cike Gurbi, Tsohon Kakakin Majalisar Bauchi Ya Dawo Majalisa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Tsohon Kakakin Majalisar dokokin jihar Bauchi, Abubakar Y. Sulaiman, da tsohon mataimakinsa Umaru Dahiru Jamilu (PDP) sun sake komawa Majalisar dokokin jihar biyo bayan nasarar da suka samu a zaben cike gurbi da ya gudana a ranar Asabar. 

Abubakar ya samu nasara ne kan babban abokin karawarsa na jam’iyyar APC, Khalid Abdulmalik.

  • Zaɓen Cike-gurbi: NNPP Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Kujeru Biyu Na Majalisar Jiha A Kano
  • Minista Idris Ya Ƙaddamar Da Ƙungiyar Kakakin Labarai 

Da yake sanar da sakamakon zaben, baturen zaben cike gurbin dan Majalisar Ningi, Farfesa Ahmad Abdulhameed ya ce Abubakar Y Sulaiman na PDP ya samu nasara ne da kuri’u 11,785 yayin da abokin nemansa na APC Khalid ya samu kuri’u 10,339.

ADVERTISEMENT

Kazalika, a mazabar cikin garin Bauchi, Hon. Umaru Dahiru Jamilu na PDP shi ne ya lashe zaben cike gurbin, inda ya samu nasarar kayar da Kwamared Aliyu Ilale na jam’iyyar APC.

Baturen zaben mazabar Bauchi cikin gari, Farfesa Isma’ila Y Shehu ya ce, Umaru Dahiru Jamilu (PDP) ya lashe zaben ne da kuri’u 45,240 yayin da Abdullahi Aliyu (APC) ya samu kuri’u. 41,266.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Umaru Dahiru dai shi ne mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi kafin kotun daukaka kara ta soke nasarar da ya samu. Da wannan matakin zai sake komawa majalisa a matsayin mamba.

Haka zancen yake a mazabar wajen garin Bauchi wato Zungur/Galambi inda baturen zaben Farfesa Adamu Samaila na jami’ar ATBU ya shelanta Hon. Yusuf Ahmed na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben mazabar da kuri’u 2,233, hakan ya ba shi nasarar kayar da abokin nemansa Ibrahim Isa Yuguda na jam’iyyar APC da ya tashi da kuri’u 1,928.

Bugu da kari, kujerar dan majalisar Madada/Chinade kuwa, Baturen zaben mazabar, Farfesa Ahmed Abdulkadir ya ayyana Ala Nasiru Ahmed na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’u 13,920 da ya mangare babban abokin nemansa na APC Dantala Ali mai samun kuri’u 9,710.

Jam’iyyar PDP da ke mulki a jihar ta Bauchi ta lashe dukkanin kujerun ‘yan majalisun da aka gudanar a zaben cike gurbi a mazabar Zungur/Galambi, Ningi, da Madara/Chinade.

Sake zaben na zuwa ne bayan da kotun daukaka kara ta soke nasarar da ‘yan majalisun hudu suka samu a zaben ranar 18 ga watan Maris na 2023. Bayan hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben mazabun, kotun daukaka kara ta umarci INEC ta sake gudanar da zabe a rumfuna 42 da suke gundumomin zabe 16 a cikin kananan hukumomi uku na Ningi, Bauchi da Katagum bayan kalubalantar nasarar su da abokan hamayyarsu suka yi.

Sai dai bayan saken zaben dukkanin wadanda aka yi jayayya a kan kujerun su sun sake dawowa.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.