• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tinubu Na Biyan Tallafin Mai Ta Bayan Fage – IMF

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Mutane Kalilan Ne Suka Sace Dukiyar Nijeriya Ta Hanyar Tallafin Mai – Tinubu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya karkashin Shugabancin Bola Ahmed Tinubu tana bayar da tallafin man fetur ta bayan fage.

Idan dai za a iya tunawa tun a ranar 29 ga Mayun 2023 lokacin da Shugaban kasa Tinubu yake jawabinsa na farko ya bayyana cire tallafin man fetur, wanda hakan ya haddasa tsadar farashin kayayyaki a cikin kasar nan.

  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta

Bayan wasu ‘yan makonni, Babban Bankin Nijeriya ya rushe tsarin canjin kudaden waje zuwa na bai daya tare da karya darajar naira, wanda hakan ya janyo darajar naira da karye.

A wannan makon ne IMF ya shawarci gwamnatin tarayyar Nijeriya kan ta cire tallafin mai da na wutar lantarki gaba daya.

Sai dai kuma wannan shawara ya hadu da suka a wurin wasu ‘yan Nijeriya wadanda suke ganin a halin yanzu ma ana farama da matsin rayuwa ballantana an sake cire tallafin mai da kuma na wutar lantarki, inda suke ganin cewa idan har gwamnati ta amince da wannan shawara, to za a shiga mawuyacin halin da ba a taba shiga a Nijeriya ba.

A kwanakin baya ne wasu rahotanni suka bayyana cewa an samu dogayen layuka a gidajen man fetur a wasu manyan buranin kasar nan, amma kuma kamfanin mai na kasa (NNPC) ya bayyana wa ‘yan kasar cewa akwai isasshen man fetur.

Bayan cire tallafin man fetura a watan Mayun 2023, farashin litar man fetur ta tashi daga naira 185 zuwa 400, yayin da daga baya a gidajen mai na NNPC ake sayar da shi kan naira 568, sauran gidajen man kuma ana  sayar da shi ne kan naira 600.

Gwamnati ta bayyana cewa farashin man zai ci gaba da sauyawa lokaci bayan lokaci bayan cire tallafin man, amma kuma litar man zai tsaya yadda yake duk da sauyawan farashin danyan mai a kasuwar duniya, wanda yake iya hawa da kuma sauka.

IMF ta ce muddin gwamnatin Tinubu ta ci gaba da biyan tallafin man fetura da na wutar lantarki, zai ci gaba da janyo hauhawar farashin kayayyaki da tsadar rayuwa.

Wani bincike ya tabbatar da cewa duk da irin ikirarin Shugaba Tinubu na cire tallafin man fetur, gwamnatin tarayya ta biya tallafin naira biliyan 169.4 a watan Agustan baya domin farashin litar man ya ci gaba da zama kan naira 620.

Sai dai kuma sau uku dillalan man fetur suna kara farashin litar a tsakanin watan Agusta zuwa Disambar 2023, inda lamarin ya tilasta musu sayar da litar man kan tsakanin naira 660 zuwa 670.

Amma gidajen mai na NNPC na ci gaba da sayar da litar man kan naira 617. Yayin da suka gidajen mai na ‘yan kasuwa har sun fara sayar da litar man kan naira 720 a wasu wurare.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa

Next Post

Dattawan Arewa Za Su Gabatar Wa Tinubu Shawarwari Kan Tattalin Arziki Da Tsaro

Related

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

11 minutes ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

1 hour ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

6 hours ago
IMF
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

6 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

7 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Dalilin Kotu Na Dakatar Da Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Tinubu

Dattawan Arewa Za Su Gabatar Wa Tinubu Shawarwari Kan Tattalin Arziki Da Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
IMF

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.