ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tinubu Na Biyan Tallafin Mai Ta Bayan Fage – IMF

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
IMF

LABARAI MASU NASABA

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

Asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya karkashin Shugabancin Bola Ahmed Tinubu tana bayar da tallafin man fetur ta bayan fage.

Idan dai za a iya tunawa tun a ranar 29 ga Mayun 2023 lokacin da Shugaban kasa Tinubu yake jawabinsa na farko ya bayyana cire tallafin man fetur, wanda hakan ya haddasa tsadar farashin kayayyaki a cikin kasar nan.

  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta

Bayan wasu ‘yan makonni, Babban Bankin Nijeriya ya rushe tsarin canjin kudaden waje zuwa na bai daya tare da karya darajar naira, wanda hakan ya janyo darajar naira da karye.

A wannan makon ne IMF ya shawarci gwamnatin tarayyar Nijeriya kan ta cire tallafin mai da na wutar lantarki gaba daya.

Sai dai kuma wannan shawara ya hadu da suka a wurin wasu ‘yan Nijeriya wadanda suke ganin a halin yanzu ma ana farama da matsin rayuwa ballantana an sake cire tallafin mai da kuma na wutar lantarki, inda suke ganin cewa idan har gwamnati ta amince da wannan shawara, to za a shiga mawuyacin halin da ba a taba shiga a Nijeriya ba.

A kwanakin baya ne wasu rahotanni suka bayyana cewa an samu dogayen layuka a gidajen man fetur a wasu manyan buranin kasar nan, amma kuma kamfanin mai na kasa (NNPC) ya bayyana wa ‘yan kasar cewa akwai isasshen man fetur.

Bayan cire tallafin man fetura a watan Mayun 2023, farashin litar man fetur ta tashi daga naira 185 zuwa 400, yayin da daga baya a gidajen mai na NNPC ake sayar da shi kan naira 568, sauran gidajen man kuma ana  sayar da shi ne kan naira 600.

Gwamnati ta bayyana cewa farashin man zai ci gaba da sauyawa lokaci bayan lokaci bayan cire tallafin man, amma kuma litar man zai tsaya yadda yake duk da sauyawan farashin danyan mai a kasuwar duniya, wanda yake iya hawa da kuma sauka.

IMF ta ce muddin gwamnatin Tinubu ta ci gaba da biyan tallafin man fetura da na wutar lantarki, zai ci gaba da janyo hauhawar farashin kayayyaki da tsadar rayuwa.

Wani bincike ya tabbatar da cewa duk da irin ikirarin Shugaba Tinubu na cire tallafin man fetur, gwamnatin tarayya ta biya tallafin naira biliyan 169.4 a watan Agustan baya domin farashin litar man ya ci gaba da zama kan naira 620.

Sai dai kuma sau uku dillalan man fetur suna kara farashin litar a tsakanin watan Agusta zuwa Disambar 2023, inda lamarin ya tilasta musu sayar da litar man kan tsakanin naira 660 zuwa 670.

Amma gidajen mai na NNPC na ci gaba da sayar da litar man kan naira 617. Yayin da suka gidajen mai na ‘yan kasuwa har sun fara sayar da litar man kan naira 720 a wasu wurare.

IMF
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

June 10, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Manyan Labarai

Babu Makarantar Da Aka Kai Wa Hari A Neja – ‘Yansanda

June 10, 2026
Next Post
Dalilin Kotu Na Dakatar Da Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Tinubu

Dattawan Arewa Za Su Gabatar Wa Tinubu Shawarwari Kan Tattalin Arziki Da Tsaro

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

June 10, 2026
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

June 10, 2026
Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

June 10, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

Babu Makarantar Da Aka Kai Wa Hari A Neja – ‘Yansanda

June 10, 2026
Kano: Hisbah Ta Tantance Mutane 720 Waɗanda Za A Yi Wa Auren Gata

Kano: Hisbah Ta Tantance Mutane 720 Waɗanda Za A Yi Wa Auren Gata

June 10, 2026
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

June 10, 2026
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

‘Yansanda Sun Kama Masu Satar Mutane, ‘Yan Fashi A Jigawa, Sun Ƙwato Makamai

June 10, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

‘Yan Bindiga Sun Yi Kwanton-Ɓauna, Sun Kashe Sojoji 7 A Kaduna

June 10, 2026
Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

June 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.