ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Arewa Za Su Gabatar Wa Tinubu Shawarwari Kan Tattalin Arziki Da Tsaro

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Arewa

Dattawan arewa a karkashin kungiyar ‘Arewa New Agenda’ (ANA) sun kimtsa tunkarar gwamnatin tarayya tare da shawarorin kan matakan da za a bi wajen magance matsalolin tsaro da matsin rayuwa, musamman a yankin arewa da ma Nijeriya baki daya.

A cewar dattawan, shawarrarin muddin aka amsa kuma aka yi amfani da su, la-shakka za su kawo karshen matsalolin da suka addabi kasar nan.

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Kashe Naira Biliyan Ɗaya Don Aikin Kiwon Lafiya Kyauta Ga Marasa Ƙarfi A Jihar
  • Za Mu Daidaita Farashin Abinci Kafin Watan Ramadan – ‘Yan Kasuwar Kano

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Yayale Ahmed, shi ne ya sanar da hakan a lokacin bude taron tattauna hanyoyin yadda za a bi wajen dakile matsalar yunwa a arewacin Nijeriya wanda ya gudana a Abuja a karshen mako.

ADVERTISEMENT

A Ado Ekiti ta Jihar Ekiti, dattijo kuma babban lauya (SAN), Afe Babalola, ya nemi Shugaban Kasa, Bola Tinubu da ya aiwatar da matakan da za su kai ga kawo karshen matsalar tattalin arziki da tsaro da ‘yan Nijeriya ke fama da su, yana mai cewa matsalolin na matukar ruguza kasar nan.

Shugaban ANA, Ahmad MoAllahyidi, shi ne ya gabatar da shawarorin ga dattawan da suka hada da tsoffin gwamnoni, Isa Yuguda, Sani Yerima, Jonathan Zwingina,  Babangida Ngoruje, tsohon shugaban ma’aikata na tarayya, Danladi Kifasi, Fatima Adams da shugaban hukumar alhazai, Jalal Arabi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ahmed ya ce, “A matsayinmu na dattawa, mun cimma matsayar gabatar da kanmu domin hidimta wa Nijeriya da kuma ganin mun ciyar da arewacin kasar nan gaba ba wai don mun karaya ba, saboda don mun kasance masu gaskiya.

“Muna son mu canza tsarinmu da dabarunmu wajen magance matsalolin da suka addabi arewacin Nijeriya.

“Nauyin da ke kanmu ba wai kawai mu ce gwamnati ba ta gudanar da aikin da ke kanta ba ne, dole ne gwamnati ta yi aiki tukuru tare da gudunmawa, dole ne gwamnati ta kasance mai daukan dawainiya ta hanyar jajircewarmu.

“Mu kungiyar ‘yan Nijeriya ne masu kishi, sakamakon wannan yunkurin namu za a sanar da jama’an da ke da karfin ikon inganta rayuwar al’umma baki daya.”

Kungiyar ANA ta ce akwai bukatar gwamnatin tarayya ta tallafa wa arewa ta hanyar aiwatar da dokar fara kasuwanci na 2022. A cewarta, wannan kai tsaye zai taimaka wa kamfanonin da suke yankin wajen gudanar da bincike, samar da horaswa da kuma fitar da kayayyaki daidai da yadda ake yinsu a duniyance.

Shugaban ANA ya ce shawarorin za su ba da damar bunkasa harkokin da suka shafi na noma da kuma taimaka wa kowace jiha da ke arewacin Nijeriya.

Arewa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Amurka

Martanin Gwamnatin Tinubu Ga PDP: Matsalar Nijeriya Ba Ta Kai Ta Kasar Venezuela Ba

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.