ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Arewa Za Su Gabatar Wa Tinubu Shawarwari Kan Tattalin Arziki Da Tsaro

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Arewa

Dattawan arewa a karkashin kungiyar ‘Arewa New Agenda’ (ANA) sun kimtsa tunkarar gwamnatin tarayya tare da shawarorin kan matakan da za a bi wajen magance matsalolin tsaro da matsin rayuwa, musamman a yankin arewa da ma Nijeriya baki daya.

A cewar dattawan, shawarrarin muddin aka amsa kuma aka yi amfani da su, la-shakka za su kawo karshen matsalolin da suka addabi kasar nan.

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Kashe Naira Biliyan Ɗaya Don Aikin Kiwon Lafiya Kyauta Ga Marasa Ƙarfi A Jihar
  • Za Mu Daidaita Farashin Abinci Kafin Watan Ramadan – ‘Yan Kasuwar Kano

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Yayale Ahmed, shi ne ya sanar da hakan a lokacin bude taron tattauna hanyoyin yadda za a bi wajen dakile matsalar yunwa a arewacin Nijeriya wanda ya gudana a Abuja a karshen mako.

ADVERTISEMENT

A Ado Ekiti ta Jihar Ekiti, dattijo kuma babban lauya (SAN), Afe Babalola, ya nemi Shugaban Kasa, Bola Tinubu da ya aiwatar da matakan da za su kai ga kawo karshen matsalar tattalin arziki da tsaro da ‘yan Nijeriya ke fama da su, yana mai cewa matsalolin na matukar ruguza kasar nan.

Shugaban ANA, Ahmad MoAllahyidi, shi ne ya gabatar da shawarorin ga dattawan da suka hada da tsoffin gwamnoni, Isa Yuguda, Sani Yerima, Jonathan Zwingina,  Babangida Ngoruje, tsohon shugaban ma’aikata na tarayya, Danladi Kifasi, Fatima Adams da shugaban hukumar alhazai, Jalal Arabi.

LABARAI MASU NASABA

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ahmed ya ce, “A matsayinmu na dattawa, mun cimma matsayar gabatar da kanmu domin hidimta wa Nijeriya da kuma ganin mun ciyar da arewacin kasar nan gaba ba wai don mun karaya ba, saboda don mun kasance masu gaskiya.

“Muna son mu canza tsarinmu da dabarunmu wajen magance matsalolin da suka addabi arewacin Nijeriya.

“Nauyin da ke kanmu ba wai kawai mu ce gwamnati ba ta gudanar da aikin da ke kanta ba ne, dole ne gwamnati ta yi aiki tukuru tare da gudunmawa, dole ne gwamnati ta kasance mai daukan dawainiya ta hanyar jajircewarmu.

“Mu kungiyar ‘yan Nijeriya ne masu kishi, sakamakon wannan yunkurin namu za a sanar da jama’an da ke da karfin ikon inganta rayuwar al’umma baki daya.”

Kungiyar ANA ta ce akwai bukatar gwamnatin tarayya ta tallafa wa arewa ta hanyar aiwatar da dokar fara kasuwanci na 2022. A cewarta, wannan kai tsaye zai taimaka wa kamfanonin da suke yankin wajen gudanar da bincike, samar da horaswa da kuma fitar da kayayyaki daidai da yadda ake yinsu a duniyance.

Shugaban ANA ya ce shawarorin za su ba da damar bunkasa harkokin da suka shafi na noma da kuma taimaka wa kowace jiha da ke arewacin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle
Labarai

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule
Manyan Labarai

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Next Post
Amurka

Martanin Gwamnatin Tinubu Ga PDP: Matsalar Nijeriya Ba Ta Kai Ta Kasar Venezuela Ba

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.