• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Arewa Za Su Gabatar Wa Tinubu Shawarwari Kan Tattalin Arziki Da Tsaro

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Dalilin Kotu Na Dakatar Da Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dattawan arewa a karkashin kungiyar ‘Arewa New Agenda’ (ANA) sun kimtsa tunkarar gwamnatin tarayya tare da shawarorin kan matakan da za a bi wajen magance matsalolin tsaro da matsin rayuwa, musamman a yankin arewa da ma Nijeriya baki daya.

A cewar dattawan, shawarrarin muddin aka amsa kuma aka yi amfani da su, la-shakka za su kawo karshen matsalolin da suka addabi kasar nan.

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Kashe Naira Biliyan Ɗaya Don Aikin Kiwon Lafiya Kyauta Ga Marasa Ƙarfi A Jihar
  • Za Mu Daidaita Farashin Abinci Kafin Watan Ramadan – ‘Yan Kasuwar Kano

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Yayale Ahmed, shi ne ya sanar da hakan a lokacin bude taron tattauna hanyoyin yadda za a bi wajen dakile matsalar yunwa a arewacin Nijeriya wanda ya gudana a Abuja a karshen mako.

A Ado Ekiti ta Jihar Ekiti, dattijo kuma babban lauya (SAN), Afe Babalola, ya nemi Shugaban Kasa, Bola Tinubu da ya aiwatar da matakan da za su kai ga kawo karshen matsalar tattalin arziki da tsaro da ‘yan Nijeriya ke fama da su, yana mai cewa matsalolin na matukar ruguza kasar nan.

Shugaban ANA, Ahmad MoAllahyidi, shi ne ya gabatar da shawarorin ga dattawan da suka hada da tsoffin gwamnoni, Isa Yuguda, Sani Yerima, Jonathan Zwingina,  Babangida Ngoruje, tsohon shugaban ma’aikata na tarayya, Danladi Kifasi, Fatima Adams da shugaban hukumar alhazai, Jalal Arabi.

Labarai Masu Nasaba

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Ahmed ya ce, “A matsayinmu na dattawa, mun cimma matsayar gabatar da kanmu domin hidimta wa Nijeriya da kuma ganin mun ciyar da arewacin kasar nan gaba ba wai don mun karaya ba, saboda don mun kasance masu gaskiya.

“Muna son mu canza tsarinmu da dabarunmu wajen magance matsalolin da suka addabi arewacin Nijeriya.

“Nauyin da ke kanmu ba wai kawai mu ce gwamnati ba ta gudanar da aikin da ke kanta ba ne, dole ne gwamnati ta yi aiki tukuru tare da gudunmawa, dole ne gwamnati ta kasance mai daukan dawainiya ta hanyar jajircewarmu.

“Mu kungiyar ‘yan Nijeriya ne masu kishi, sakamakon wannan yunkurin namu za a sanar da jama’an da ke da karfin ikon inganta rayuwar al’umma baki daya.”

Kungiyar ANA ta ce akwai bukatar gwamnatin tarayya ta tallafa wa arewa ta hanyar aiwatar da dokar fara kasuwanci na 2022. A cewarta, wannan kai tsaye zai taimaka wa kamfanonin da suke yankin wajen gudanar da bincike, samar da horaswa da kuma fitar da kayayyaki daidai da yadda ake yinsu a duniyance.

Shugaban ANA ya ce shawarorin za su ba da damar bunkasa harkokin da suka shafi na noma da kuma taimaka wa kowace jiha da ke arewacin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Har Yanzu Tinubu Na Biyan Tallafin Mai Ta Bayan Fage – IMF

Next Post

Martanin Gwamnatin Tinubu Ga PDP: Matsalar Nijeriya Ba Ta Kai Ta Kasar Venezuela Ba

Related

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja
Manyan Labarai

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

1 hour ago
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
Labarai

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

2 hours ago
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata
Labarai

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

3 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

4 hours ago
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

18 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

22 hours ago
Next Post
Amurka

Martanin Gwamnatin Tinubu Ga PDP: Matsalar Nijeriya Ba Ta Kai Ta Kasar Venezuela Ba

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

August 10, 2025
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.