ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Martanin Gwamnatin Tinubu Ga PDP: Matsalar Nijeriya Ba Ta Kai Ta Kasar Venezuela Ba

by Sulaiman
2 years ago
Amurka

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce duk da yake tattalin arzikin Nijeriya na fuskantar ƙalubale, kwatanta shi kafaɗa-da-kafaɗa da na Venezuela da gwamnonin jam’iyyar PDP su ka yi rashin adalci ne.

Ya ce: “Mu na bayyana cewa, duk da yake ƙasarmu na fuskantar wasu matsaloli, waɗanda kuma wannan gwamnati ta Shugaba Tinubu na ƙoƙarin magancesu, amma matsalolinmu ko kusa ba su kai irin na kasar Venezuela ba, kamar yadda gwamnonin PDP su ka yi zargi.”

  • Adadin Zirga-zirgar Fasinjoji A Jiragen Kasa Ya Zarce Miliyan 230 A Rabin Farko Na Wa’adin Hutun Bikin Bazara
  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, ministan ya ce: “Tattalin arzikin Nijeriya har yanzu ya na da ƙarfi sosai, kuma ana sa rai da kyakkyawan hasashen cewa zai bunƙasa da ƙarin kashi 3 cikin 100 cikin wannan shekarar.

ADVERTISEMENT

“Tattalin arzikin mu na bayar da gudunmawar lamuni ga masu rance a cikin gida da waje.”

A ranar Litinin ne Gwamnonin PDP su ka gudanar da taro a Abuja, inda suka tattauna batutuwa, musamman waɗanda su ka shafi matsalar tsaro da matsalar tattalin arziki, wacce ta haifar da tsadar rayuwa.

LABARAI MASU NASABA

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

Bayan kammala taron, sun bada sanarwar cewa, sun amince kowace jiha a ba ta damar kafa ‘yansandan jiharta, domin shawo kan ƙalubalen matsalar tsaro a faɗin ƙasar nan.

Amma a martaninsa, Ministan ya ce, “Mu na maraba da shawarwarin da su ka bayar waɗanda ba na son rai ba, domin ganin an magance matsalolin tsaro da na tattalin arziki.

“A matsayinsu na shugabanni a gwamnatocin jihohi, gwammonin PDP su na da ‘yancin bayyana matsayarsu kan duk wani abu da ya shafi ƙasar nan.

“A matsayin gwamnonin PDP, waɗanda ya kamata a ce masu shiga sahun gaba ne kan inganta tattalin arziki, samar da yalwa a ƙasa da al’ummar jihohinsu, a ce kuma sun koma su na furta kalaman ƙage da shaci-faɗi kan Nijeriya, har su na kwatanta matsalar tattalin arzikin Nijeriya da irin matsalolin da su ka dabaibaye tattalin arzikin Venezuela.

“Mu na son mu bayyana cewa duk da yake dai tattalin arzikinmu na fuskantar ƙalubale, amma ko kusa ba daidai ba ne a kwatanta matsalar Venezuela da ta Nijeriya.

“Yayin da Gwamnatin tarayya ke biyan albashi da sauran haƙƙoƙin ma’aikata kan kari, kuma harkokin gwamnati na tafiya daidai-wa-daida, ya kamata ‘yan Nijeriya su tambayi gwamnonin PDP abin da su ka yi da kuɗaɗen da ake ba su.

“Saboda akwai rahoton bincike mai nuna cewa, yawancin jihohin PDP sun kasa biyan ‘yan fansho kuɗaɗensu na tsawon watanni da dama, haka albashin ma’aikata ma wasu ba su biya yadda ya kamata.

“Gwamnonin PDP na ƙin biyan garatutin ma’aikatan da su ka yi ritaya.

“Haka kuma wasu gwamnonin PDP ɗin har yau sun kasa biyan naira 30,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi, shekaru huɗu da Gwamnatin Tarayya ta fara amfani da tsarin.”

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026
  • Sulaiman
    Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

MASU ALAKA

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi
Labarai

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

June 10, 2026
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

June 10, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Next Post
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

LABARAI MASU NASABA

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

June 10, 2026
An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

June 10, 2026
Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

June 10, 2026
An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

June 10, 2026
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

June 10, 2026
Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

June 10, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

Babu Makarantar Da Aka Kai Wa Hari A Neja – ‘Yansanda

June 10, 2026
Kano: Hisbah Ta Tantance Mutane 720 Waɗanda Za A Yi Wa Auren Gata

Kano: Hisbah Ta Tantance Mutane 720 Waɗanda Za A Yi Wa Auren Gata

June 10, 2026
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

June 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.