• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Muhammad Sanusi, ya ce, a maimakon dora laifin halin kunci da matsatsi rayuwa da ake ciki a Nijeriya ga Shugaban kasa, Bola Tinubu, zarge-zargen da tuhume-tuhumen kai har ma da nuna yatsar, ya kamata ne a yi su kan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, kan yadda ya bi wajen janyo matsaloli ga tattalin arziki.

Tsohon sarkin Kano, wanda ke jawabi ta tangaraho a ranar Lahadi a wajen wani taron addini da ya gudana a Abuja, ya ce tsohon gwamnatin da ta gabata ta kasa gudanar da tsare-tsaren da za su taimaka wa tattalin arziki.

  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta

A cewarsa, Buhari ya toshe kunnuwansa kan yadda za a bi wajen magance matsalolin da suka shafi tattalin arzikin kasar nan.

Ya ce, shi kam ba zai biye wa wasu gungun ‘yan Nijeriya da suke son ya soki Shugaban kasa Tinubu kan halin kunci da ake ciki a kasar nan ba.

Sanusi ya ce, “Tsawon shekaru na sha fada kan cewa za a fada matsalolin tattalin arziki. Dukkanin wani masanin tattalin arziki da ya fahimci yadda aka bi da tattalin arzikin kasar nan a shekaru takwas da suka wuce ya san za a iya tsintan kai cikin irin wannan mawuyacin yanayin.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

“Wannan kuncin rayuwa da ‘yan Nijeriya ke fuskanta, yanzu ma aka fara shiga muddin ba a dauki matakan da suka dace ba, saboda Nijeriya ba ta kasance wata kasa ta daban ba, irin wannan yanayin ya faru a Jamus, Zimbabwe, Uganda, da Benezuela.

“Tsohon gwamnati ta toshe kunnuwarta ta ki sauraron rokonmu kan matakan da za a bi a kan tsarin tattalin arziki. Na fada a gaban shugaban kasan da ke mulki a yanzu a Jihar Kaduna, cewa duk wani dan siyasan da ya gaya muku cewa abubuwa za su yi sauki, kar ma ku zabeshi, saboda karya yake muku. Mutane sun yi watsi da shawarwarinmu ne da tunanin kawai maganace ake yi ta siyasa.

“Idan zan yi adalci ga Shugaba Bola Tinubu, ba shi ne ya dace a dora wa alhakin matsatsin da ake ciki ba a halin yanzu, sama da shekaru takwas muna rayuwa ciki tsari irin ta karya da lafto basuka daga kasashen waje da ya wuce hankali.

“Ba zan shiga a dama da ni ba wajen sukar Tinubu kan matsatsin rayuwa da ake fuskanta a yanzu ba, ba wai ina cewa shi din ba zai iya yin kuskure ba ne, amma a dai wannan matsatsin da ake ciki, shugaban kasa Tinubu bai da laifi. Zan yi magana muddin na ga wani kuskure a tsarin tattalin arzikin gwamnatin Tinubu a nan gaba.” Sanusi ya shawarci masu hannu da shuni da su taimaka wa wadanda ba su da shi a halin da ake ciki tare da neman jama’a da su kara hakuri. Sannan, ya shawarci jama’a da su rage buri da dora wa kai abubuwan da ba su wajaba ba domin samun rayuwa cikin sauki da samun abincin da za a ci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Martanin Gwamnatin Tinubu Ga PDP: Matsalar Nijeriya Ba Ta Kai Ta Kasar Venezuela Ba

Next Post

Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

11 minutes ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

41 minutes ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

4 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

7 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

7 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

17 hours ago
Next Post
Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.