• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Mata Ta Taba Zagina A Kan Littafina ‘Umarnin Uba’ —Yareema Shaheed

by Primcess Fatima Zarah Mazadu
2 years ago
Yareema

Daya daga cikin marubuta littattafan Hausa na yanar gizo, YAREEMA SHAHEED ya bayyana wa masu karatu wasu batutuwa da suka faru da shi sanadiyyar rubutu, tare da bayyana irin gwagwarmayar da ya sha kafin ya fara rubutu.

Ga dai tattaunawa tare da PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU kamar haka:

Ya sunan malamin?

Sunana Yareema Shaheed (Abou Hashmat).

Ko za ka fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinka?

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

An haife ni a garin Kaduna, na yi karatun firamare da sakandare duk a garin Jos, na je Katsina na yi karatun kiwon lafiya.

Me ya ja hankalinka har ka fara rubutu?

Abin da ya sa na tsunduma rubutu dan in fadakar tare da ilmantarwa.

Kamar wanne bangare kafi mayar da hankali a kai wajen yin rubutu?

Na fi mayar da hankalina kan zamantakewa da sarauta da dai sauransu.

Ya gwagwarmayar fara rubutun ya kasance?

Na sha wuya lokacin da na fara rubutu, domin na bibiyi manyan marubuta su saka ni a hanya wasu suka dinga yawo da hankalina, hakan ya sa na tsunduma rubutu da kaina a karshe makaranta suka karbe ni hannu bibbiyu.

Lokacin da iyayenka suka fara sani, shin ka samu wani kalubale daga gare su?

Eh! To, gaskiya na dan samu matsala kadan, saboda ni na fito daga gidan sarauta.

Daga lokacin da ka fara rubutu zuwa yanzu ka rubuta labari ya kai kamar guda nawa?

Na rubuta littattafai da yawa daga ciki akwai; Umarnin uba, Aure nake so, Saurayina Ne Sila, Hawayen Jini, Shaheed da Shaheedah, My Destiny, Maisara da sai sauransu.

Ka taba buga labarinka cikin labarun daka rubuta?

Na taba buga ‘Mu bi iyaye’.

Wanne labari ne ya zamo bakandamiyarka cikin wanda ka rubuta?

Hawayen Jini, Shaheed da Shaheedah.

Wanne irin nasarori ka samu game da rubutu?

Nasarorin dana samu ba zan iya lissafawa ba, rubutu ya kaini inda ban taba zatan zan je ba.

Wanne irin kalubale ka taba fuskanta game da rubutu?

Akwai wata mata ta taba kirana cikin dare tana zagina akan littafin UMARNIN UBA, wai na ci zarafin tauraruwar labarin, har da kukanta sosai.

Ya ka dauki rubutu a wajenka?

Na dauki rubutu a matsayin sana’a da kuma hanyar da zan isar da sako cikin sauki.

Mene ne burinka na gaba game da rubutu?

Burina na kara suna a duniyar rubutu, na kai inda ban zata ba.

Wanne abu ne ya taba faruwa da kai na farin ciki ko akasin haka wanda ba za ka taba iya mantawa da shi ba?

Ina tuna ranar da ina tafiya zuwa Abuja a cikin mota na ji fasinjas mata suna fira akan littattafana, ba su san ni ne ba, har tana cewa; “YAREEMA SHAHEED ai yana ban mamaki wajen rubutu sai ka ga kamar an zo karshe sai kuma ka ga an ci gaba, ke ni fa na dauka mace ce marubuciyar, ashe namiji ne. Ina mamakin yadda yake fitar da komai a gurin daya da ce, na gaishe da gwarzo”.

Bayan rubutu kana sana’a?

Ni likita ne.

Ya ka ke iya hada rubutunka da kuma aikinka?

Kowanne na ware masa lokacinsa.

Kamar da wanne lokaci ka fi jin dadin yin rubutu?

Da yamma ko lokacin da nake tafiya ko nake cin abinci.

Me za ka ce da masu karanta labaranka?

Ina kira ga makaranta labarina cewa; nan da ranar Juma’a zan fara sakin sabbin littattafaina guda biyu; Katangar Sikari, Matan Fada.

Ko kanada wadanda za ka gaisar?

Ina gaida Maimartaba Sarkin Kano da Matata Uwar ‘Ya’yana Ummu Hashmat, ina gaida Zainab Sulaiman Zeety, ina gaida Gimbiya Rahma, ina gaida Muhammad Adam Sameeru.

Muna godiya

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)
Adabi

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

April 19, 2025
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

December 30, 2024
Next Post
Kotu Ta Bai Wa Emefiele Damar Yin Tafiye-tafiye A Nijeriya

Zargin Badakala: Emifiele Ya Sake Shiga Tsaka Mai Wuya Kan Dala Miliyan 6

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.