ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

Mutane da dama ne suka taya Dr. Maryam Mansur Yola murnar zama Farfesa kan magungunan gargajiya da al'adu a shafukan sada zumunta.

by Muhammad and Naziru Adam Ibrahim
1 year ago
Dr

Majalisar Gudanarwar Jami’ar Bayero da ke Kano, ta amince da ɗaga darajar Dr. Maryam Mansur Yola, ta Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, da ke Jami’ar zuwa matsayin Farfesar Magungunan Gargajiya da Al’adu, kamar yadda wata sanarwa da Jami’ar ta fitar a ranar Juma’a 27 ga Disamba, 2024 ta bayyana.

Farfesa Maryam Yola, ‘yar asalin ƙaramar hukumar Kano Municipal, ita ce mace ta farko a tarihi da ta zama farfesa kan magungunan gargajiya da al’adun Hausa, kuma malama ce da ke koyar da kwasa-kwasan Al’adun Bahaushe da ta koyar da ɗumbin ɗalibai a matakan ilimin daban-daban a ciki da wajen Nijeriya.

  • Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani
  • Za Mu Sabonta Dakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita

Farfesa Yola, mace ce da ta yi fice kan bincike a fannin magungunan gargajiya tun daga digirinta na farko, inda ta yi akan darussan Hausa a shekarar 1990, ta yi digirinta na biyu kan al’adun Bahaushe a shekarar 1997. Farfesa Yola ta kuma kammala karatunta na digiri na uku a shekara ta 2017, duka a Jami’ar Bayero. Kazalika, Farfesar ta yi babbar difiloma kan harkokin koyar da ilmi (PDE) a Kwalejin Shari’a ta Malam Aminu Kano (Legal) da ke Kano, inda ta kammala a shekarar 2015, ta kuma samu ƙarin wasu takardun shaidar ilimi a wasu kwasa-kwasai da dama.

ADVERTISEMENT

Baya ga takardu da maƙalu masu tarin yawa da ta gabatar kan magungunan gargajiya a jami’o’i da makarantu da wuraren tarukan ilimi daban-daban a ciki da wajen Nijeriya, ta duba aikin ɗalibai masu tarin yawa a matakin digiri na ɗaya da na biyu da na uku a Jami’ar Bayero da wasu Jami’o’i a Nijeriya.

Farfesa Yola, ta kuma riƙe muƙamai da dama a matakin gwamnatin tarayya da jiha da wasu kungiyoyin siyasa da jami’a da ƙungiyoyin ci gaban al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Farfesa Mansur Yola, mamba ce a Ƙungiyar malaman Jami’o’i ta ƙasa (ASUU), kazalika mamba ce a Ƙungiyar Mata ta (ASFECOM), da kuma hukumar da ke bayar da shaidar malanta ta Nijeriya (TRCN).

A zamanin mulkin Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau, ta riƙe Shugabar Hukumar Ilimin bai-ɗaya ta Jihar Kano daga 2008 zuwa 2011, da sauran muƙaman gwamnati da siyasa da dama a matakai daban-daban.

Ana sa ran ɗaga darajar Fafesar zuwa wannan mataki zai ƙara mata himma da ƙwarin gwuiwar ci gaba da bayar da gudunmowa wajen inganta harkokin magungunan gargajiya a Nijeriya, ta hanyar amfani da ɗimbin ilimi da ƙwarewarta a fannin, tare da bunƙasa al’adun Hausa, da cike giɓin da ake da shi a ɓangarorin magungunan gargajiya da al’adun Hausa.

Dr
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje
Dr
Naziru Adam Ibrahim
+ posts Bio
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Shugaba Tinubu Ya Isa Nairobi Domin Halartar Taron Tattalin Arzikin Nahiyar Afirka
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Gwamnatin Filato Ta Kwato Kadarorin Jihar Da Aka Wawashe
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    DSS Da Jami’an Kotu Sun Kori Ƴan Jarida Daga Ɗakin Shari’a A Abuja
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Zaɓen 2027: APC Na Iya Hana Mu Yin Kamfen – Buba Galadima

MASU ALAKA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Next Post
Yankin Xinjiang Na Kasar Sin Ya Kammala Aikin Shimfida Rami Mafi Tsawo A Duniya

Yankin Xinjiang Na Kasar Sin Ya Kammala Aikin Shimfida Rami Mafi Tsawo A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.