ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

by Adamu Yusuf Indabo
1 year ago
Batsa

Fitacciyar marubuciyar littattafan Hausa, ‘yar asalin Zinder da ke Jamhuriyar Nijar, wacce aka fi sani da Emilia. Ta yi wannan kira ne ga ‘yan uwanta marubuta da su sanya tsoron Allah a cikin rubuce-rubucensu musamman ma dai marubutan batsa, wadanda ta ce suna warware tufkar da sauran managartan marubuta ke tufkawa da badalar da suke yada wa duniya. Marubuciya Emilia dai ta yi wannan kira ne a yayin tattaunawarta da wakilin LEADERSHIP Hausa, wato Adamu Yusuf Indabo. Ga dai cikakkiyar tattaunawar tasu kamar haka:

To farko mene ne cikakken sunanki, da kuma takaitaccen tarihin rayuwarki?

  • Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano
  • Bukatar Kawo Karshen Mamayar Da Kamaru Ke Yi Wa Yankunan Nijeriya

Sunana Zouley Sabitou. An haife ni 23 ga watan Afrilu a shekara 2003 a garin Yékoua ce da ke jahar Zinder/Damagram, na yi nursery a garin Arlit da kuma aji biyu na primary, na yi sauran primary da secondry a garin Agadez da kuma karatun addini duk a nan Agadez, ina Unibersity ne a garin Dosso. Enbironnement et numérikue nake karantawa a Unibersity duk da dai na yi karatun likitanci yanzu kam sai na koma harkar gonaki da muhalli.

ADVERTISEMENT

To sunan Emilia da kowa ya san ki da shi, ina ya samo asali?

Sunan zouleyha kakana ne ya saka min shi to daga baya mahaifina ya canza min suna yana kira na ne da Émilia har kuma sunan ya bi ni wanda har Zouley din kan yi nisan kiwo.

LABARAI MASU NASABA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

To mun san ki a matsayin marubuciyar littafan Hausa. Shin ta ya kika tsinci kanki a duniyar rubutu?

Hukuncin Ubangiji, na yi karance-karance da dama a baya, tun ina karamar secondary na fara rubuta labari a paper a shekarar 2016, idan na rubuta sai na ajiye. Lokacin da muka yi hutu da aka dawo aji na Hudu (a kasar Nijar shekara 4 muke yi a karamar secondary) a karamar secondary a lokacin na fara karantawa kawayena, idan an yi break, to bayan na gama karama secondry na ci gaba da rubutun a paper, a shekara ta 2019 na fara rubutu a yanar gizo har na fara yadawa.

A 2016 mene sunan littafin da kika fara rubutawa?

Gaskiya ba zan iya tunawa ba, don a lokacin ban wani kware a rubutu ba, bayan na gama karanta musu na kan nemi shawararsu a kan yadda labarin zai ci gaba ko abin da ya dace na canza ko sunan da ya dace da labarin.

To wanda kin fara yadawa a yanar gizo cikin shekaran 2019, wanne littafi ne?

Khairat: sunan littafin da na fara fitarwa a 2019 shi ne KHAIRAT. Labarin ya ginu ne don jan kunne ga irin iyayen da suke nacewa sai ‘ƴarsu ta yi karatu kuma a kasashen waje, sai a yi rashin sa’a ita kuwa yarinyar aure take son yi, daga nan rayuwar yaran za ta iya lalacewa, duk da ita Khairat din a nata bangaren ta yi aure ne a boye ba tare da sanin iyayenta ba a kasar da suka aika ta karatu. To bayan Khairat kuma zuwa yanzu na yi wasu littafan guda (14) har da shi ya zama ina da littafai (15) ke nan da na fitar, kuma dukkansu a yanar gizo. Littafan guda Goma Sha Biyar kuwa su ne: Khairat, Nazi’at, Na Yi Asara, Babbar ‘Yar Duniya, Dan Kuka, Mutuwar Aure, Samha, Tura Ta Kai Bango, Gudun Tsira, Dambarwar Aurensu, Dambarwar Abin Dake Raina, Kuskure, Da Wata Kusan, Abin Dake Boye, Kwakwalwar Kifi.

A cikin wadannan littafai guda 15, wanne ne bakandamiyarki?

Labarin ‘Kuskure’ shi ne bakandamiyata. Labari ne da aka gina shi a kan gudun son zuciya, cire kiyayyar wani mutum a rai saboda ba ka san abin da gobe za ta haifar ba. Don gaba da kiyayya ba su da amfani, kuma Manzon Rahama ma ya hane mu a kan zurfafawa a cikin kiyayya.

Kika ce a baya kin yi karance-karancen littafan Hausa. To cikin marubuta na wancan lokacin wace ce gwanarki?

To ai ni har yanzu ban daina karance-karancen Hausa ba. Duk da asalin marubutan sun daina rubutun zube, amma an samu sabbin marubuta. A da gwanata ita ce marubuciya Fauziyya D Sulaiman. A yanzu kuwa zabin tilo a cikin marubuta gare ni zabi ne mai wahala. Sai dai zan iya cewa: a bangaren zamantakewa marubuciya ‘Billyn Abdul’ ce gwanata, idan kuma bangaren horror sai na ce ‘Chamsiya Laouli Rabo’ idan kuma littafin yaki ne to marubuci ‘Mansur Usman Sufi’.

To ko cikin marubuta kina da kawa shakikiyar da kowanne lokaci za a iya samun labarin halin da keki ciki a wajenta?

Kwarai ina da Aunty Fa’iza Abubakar wadda aka fi sani da Maman Afrah.

To ya batun kungiyar marubuta?

Ina cikin kungiyar First Class Writer’s Association wadda tun farkon fara rubutuna antyna Rahama Sabo Usman ita ce ta saka ni a cikinta.

To a matsayinki na tsohuwar makaranciya, ya za ki kimanta marubutan da da kuma na yanzu ta fuskar kwarewa da ilimantarwa?

Babu hadi gaskiya domin kowa akwai matsayinsa, marubutan da sun yi rubutu ne a kan matsalolin da suka shafi al’umma a da, su kuwa marubutan yanzu suna rubutu ne a kan abin da ta shafe mu yanzu, duk da dai yanzu bin ka’idodi da dokokin da adabi ta tanadar ya yi karanci fiye da da can baya saboda yanzu duk wanda ya ga dama zai iya zama marubuci, sai kuma baragurbin marubuta wato marubutan batsa da suka yi yawa a halin yanzu wanda muna tufka su kuwa suna warware wa ne.

To ya batun shiga gasar rubutu?

A duk lokacin da zan ji labarin gasar rubutu bana kasa a guiwa wajen shiga, wasu an yi nasara wasu kuwa ba a yi ba, duk da dai iya shiga gasar ma nasara ce babba. Gasar da na yi nasara kuwa. Akwai gasar da aka shirya a lokacin bikin marubuci Yareema Shaheed gaskiya na manta sunan gidan tb da suka shirya gasar. Sai gasar da kungiyar raya al’adu ta jihar Gombe suka shirya.

Kuma a wanne yanayi ko lokaci kika fi jin dadin yin rubutu?

A duk lokacin da na ci na koshi bana kuma tare da gajiya, sha’awar yin rubutun kan zo mini.

To wadanna nasarori kika cimma a rayuwa ta sanadiyyar rubutu?

Na farko babbar nasara ta ita ce haduwa da mutanen kirki wanda a halin yanzu suke tamkar ‘yan uwana kama daga marubuta har makaranta.

Nasara ta biyu kuma harkar rubutu na saka ni alfahari don a duk inda zan shiga bana jin shakkar kiran kaina da marubuciya. A yanzu kuma bayan fadakarwar da nake yi ina daukar harkar rubutu a matsayin hanyar da zan samu dan na kashewa saboda bunkasar tattalin arzikina.

To wanne kalubale kika fuskanta bayan shigowar ki duniyar rubutu?

Da farko dai kalubalen da na fuskata daga mahaifiyata ne don ina fama da matsalar ciwon ido a lokacin idan na zauna na fara rubutun a waya ko laptop, za ta rika faka a kan ba ki da lafiya amman kullum kina jone da wannan screen ɗin don yin rubuce-rubuce, amman daga baya da rashin lafiyar ya yi sauki sai kawai ta daina mita tana yi min fatan alkairi. Kalubale na gaba kuwa ina son makaranta su rika yi min comment a duk bayan da suka karanta labarina sai dai kuma ba sa yi sai an kai ruwa rana.

Ko wanne kira za ki yi ga ‘yan uwanki marubuta?

Kirana ba zai wuce mu ji tsoron Allah a duk sanda za mu kaura alkalami ba, mu rubuta abin da zai anfane mu ya anfani al’umma, abin da ko da an tambaye ki gobe ba za ki yi da-na-sanin rubuta shi ba, kuma abin da ko ‘ƴarki ko kawarki za ki iya bari ta karanta. Sannan mu rike zumunci da karfafa juna ta hanyar karawa juna sani a duk lokacin da bukatar hakan ta taso, domin duk inda marubuci yake to fa dan uwanmu ne. Sai kuma marubutan batsa ku ji tsoron Allah.

To wanne sako kike da shi ga masoyanki da suke bibiyar rubuce-rubucenki?

Ina yi wa duk wani masoyina fatan alkairi, da fatan Allah Ya biya masa bukatunsa na alkairi kuma ina mai farin cikin sanar da su zan ci gaba da fadakar da su da kuma nishadantar da su gwargwadon iyawata.

To Hajiya Emilia muna godiya.

Ni ce da godiya.

Batsa
Adamu Yusuf Indabo
+ postsBio
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    An Yi Yekuwar Daukar Matakin Gaggawa Kan Take ‘Yancin ‘Yan Jarida
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubutan Da Akwai Hikima, Na Yanzu Sai Karyar Zuwa Waje – Amina
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Ba Nanaye Ko Rashin Da’a Nake Rubutawa Ba – A.S Aikawa
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubuta Tamkar Madubi Suke Ga Al’ummah – Zainab Salihu Yarima

MASU ALAKA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso
Adabi

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

February 6, 2026
CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki
Adabi

CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

January 30, 2026
Next Post
Ba Na Goyon Bayan Dakatar Da Gwamnan Jihar Ribas – Ndume

Ndume Ya Yaba wa Sojoji Kan Daƙile Harin Boko Haram A Gwoza

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.