• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Ortom Ya Bukaci A Saki Jagoran IPOB Nnamdi Kanu

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gwamna Ortom Ya Bukaci A Saki Jagoran IPOB Nnamdi Kanu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Binuwai, ya yi kira da a sake Shugaban haramtacciyar kungiyar gwagwarmayar kafa yankin Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu, da ake tsare da shi a halin yanzu domin daukar matakin zaman lafiya da muhimmancin gaske a kasar nan.

Gwamna Ortom ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya amshi bakwancin wasu ‘yan asalin Igbo karkashin ‘American Veterans of Igbo Origin’ da suka kai masa ziyarar a Washington DC, da ke kasar Amurka ranar Laraba.

  • Okupe Ya Janye A Matsayin Dan Takarar Mataimakin Jam’iyyar Labour Ta Peter Obi

Ya ce, batun Kanu kalubale ne da ya shafi zamantakewa da siyasa don haka akwai bukatar tafiyar da lamarin cikin siyasa domin shawo kan kalubalen.

Gwamnan ya ce hatta mambobin Boko Haram da suka zama barazana ga tsaron kasa ana samun wadanda aka ‘yantasu har ma su koma cikin al’umma tare da zargi cewa har ma shiga aikin soja su na yi.

Gwamna Ortom ya ce akwai bukatar bai wa yankin Kudu Maso Gabas damar jin an tare da su ta hanyar sauraron kullin da ke ransu na ganin wariya ga wani bangare a kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Ya jawo hankalin tsoffin ‘yan Igbo da suke zaure a Amurka da su cewa Nijeriya daya ce, ya duk duniya babu kasar da bata da kalubalen da ke damunta.

Ortom ya shaida wa kungiyar cewa mulkin Nijeriya zai dawo yankin Kudu Maso Gabas ne kawai idan al’ummar yankin suka jingine banbance-banbancensu waje guda suka hada kai domin cigabansu.

Gwamnan ya gode wa kungiyar a bisa gudunmawar da suke bayarwa ya kuma nemi da su cigaba da bada gudunmawarsu wajen kyautata zaman lafiya a Nijeriya.

Kungiyar a karkashin jagorancin Shugabanta Dakta Sylvester Onyia, da mataimakinsa Dakta Prince Joe Nduka.

Sauran mambobin da suka kai ziyarar sun hada da Dr Ofo, Kakakin kungiyar, tsohon Jakadan Nijeriya a Afirka ta Kudu Dr Mrs Ajulu.

Onyia ya jinjina wa Ortom a bisa kokarinsa, ya nuna cewa irin su Ortom Nijeriya take bukata a matsayin shugabanni. Ya ce, duk da suna kasar waje amma suna nazartar abubuwan da suke faruwa a Nijeriya.

Daga nan ya nuna fargana kan zaben 2023 da cewa matsalolin tsaro da suke faruwa a Nijeriya kada su kai ga kawo matsala ga babban zaben.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

IPOB Ta Yi Barazana Ga Jakadiyar Birtaniya A Nijeriya

Next Post

Ya Kamata A Kafa Kotun Hukunta Masu Cin Hanci Da Rashawa Ta Duniya – Buhari

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

1 hour ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

3 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

8 hours ago
Ortom
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 hours ago
Next Post
Ya Kamata A Kafa Kotun Hukunta Masu Cin Hanci Da Rashawa Ta Duniya – Buhari

Ya Kamata A Kafa Kotun Hukunta Masu Cin Hanci Da Rashawa Ta Duniya - Buhari

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.