• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Gidajen Bahaya Sun Kara Farashi Da Kaso 100 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Bahaya

Kungiyar masu gidajen Bahaya a karamar hukumar Bauchi sun kara kudin da suke amsa a wajen masu yin fitsari, ba-haya (bayan gida) da wanka zuwa kaso 100.

Malam Ibrahim Kabo, shugaban kungiyar ne ya sanar da hakan a hirarsa da kamfanin dillacin labarai na kasa a Bauchi ranar Alhamis.

  • Gwamna Dikko Umar Ya Taya Kwamarad Dan Ali Murnar Zama Shugaban NUJ Mafi Kwazo A Arewa Maso Yamma.
  • Wakilin Sin: Kuri’ar Kin Amincewar Da Amurka Ta Jefa Kan Kudurin Tsagaita Wuta A Gaza Ta Rushe Matsayar Kwamitin Sulhun MDD

A cewarsa, sauyin farashin kudin ya kama naira 200 ga duk mai son yin bahaya a maimakon naira 100 da ake biya a baya, sannan kudin wanka da ruwan zafi ko na sanyi ya tashi daga naida 100 zuwa naira 200.

Kabo ya yi bayanin cewa, dole ce ta sanya su daukan matakin kara kudin zuwa hakan sakamakon yadda kayayyakin da suke amfani da su wajen kula da ban-daki suka yi tsada matuka.

“Muna amfani ne da sabulu, sinadarin wanke bayan gida (detergent), maganin kashe kwayoyin cuta, fetur, man tsaftace hammata ko matse-matsi, bokitaye, tsintsiya, abubuwan zubar da shara, tsunmar share datti (toilet paper) da sauran muhimman abubuwan da muke amfani da su a gidajen wankanmu domin gamsar da jama’a su samu kwanciyar hankalin biyan bukatunsu.

LABARAI MASU NASABA

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

“A gefe guda kuma, mun kara kudin da muke biyan ma’aikatanmu ladar wahalarsu, rawar da suke takawa na da matukar muhimmanci saboda su ne ke kula da tsaftace gidajen Bahaya da kula da su.

“Wadannan dalilan su ne suka haddasa karin kudin zagayawa da na wanka a gidajen Bahaya da suke kwaryar cikin gari,” inji Kabo.

Ya ce a matsayinsu na masu gangamin wayar da kai wajen ganin an dai kashi (tutu) a bainar jama’a, dole ne kuma Mambobin kungiyarsu su kara farashi domin ba su damar iya biyan kudaden da suka dace kuma suka wajaba sannan su cigaba da gudanar da sana’ar ta su.

Da ya ke tofa albarkacin baki kan wannan lamarin, wani kwastoma mai amfani da gidajen ba-haya, Aliyu Danjuma, ya nuna damuwarsa kan karin, amma bai daura wa masu mallakin gidajen ba-haya din laifi ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Manyan Labarai

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
Labarai

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Manyan Labarai

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

November 2, 2025
Next Post
Wakili Ya Rasu Kwana 3 Da Karewar Wa’adinsa A Matsayin Dan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi

Majalisar Dattawa Ta Buƙaci Gwamnati Ta Janye Shirin Ƙara Kuɗin Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

November 2, 2025
An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

November 2, 2025
Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Maganin Nankarwa (3)

Maganin Nankarwa (3)

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.