• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilin Sin: Kuri’ar Kin Amincewar Da Amurka Ta Jefa Kan Kudurin Tsagaita Wuta A Gaza Ta Rushe Matsayar Kwamitin Sulhun MDD

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Wakilin Sin: Kuri’ar Kin Amincewar Da Amurka Ta Jefa Kan Kudurin Tsagaita Wuta A Gaza Ta Rushe Matsayar Kwamitin Sulhun MDD
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin sulhu na MDD ya kada kuri’a game da daftarin kudurin tsagaita wuta a Gaza nan da nan, wanda kasar Aljeriya ta gabatar a madadin kasashen Larabawa, to sai kuma ba a zartas da kudurin ba sakamakon kuri’ar kin amincewar da Amurka ta jefa.

Zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Zhang Jun, ya jefa kuri’ar amincewa da kudurin, kana ya ba da jawabi don bayyana matsayin bangaren Sin. Zhang Jun ya ce bangaren Sin ya yi bakin ciki sosai game da yadda Amurka ta ki amincewa da daftarin.

  • Cibyar Dakon Kaya Da Kasar Sin Ta Gina Na Taimakawa Bunkasar Kayayyakin Da Ake Fitarwa A Kasar Uganda
  • Don Tabbatar Da Adalci A Duniya Ana Bukatar Hadin Gwiwar “Global South”

Daftarin kudurin da Aljeriya ta gabatar a madadin kasashen Larabawa, na bukatar tsagaita wuta a Gaza nan da nan, da saki dukkan mutanen da ake tsare da su, da shigar da kayayyakin jin kai, da kuma hana tilastawa jama’a canja matsuguni, wannan ba ma kawai bukata ce ta gaggawa game da yanayin da ake ciki a yanzu ba ne, har ma yana da alaka da samar da abubuwan bukatun jin kai, don haka ya kamata dukkan mambobin kwamitin sulhun su nuna goyon baya ga kudurin.

Sakamakon jefa kuri’un ya nuna cewa, kwamitin sulhun MDD ya cimma matsaya guda daya kan batun, amma Amurka ta rushe matsayar. Ya ce matakin na Amurka ya jefa Gaza cikin yanayi mai hadari.

A yayin jefa kuri’ar ta wannan karo, daftarin kudurin da Aljeriya ta gabatar ya samu kuri’un amincewa 13, ciki har da kuri’ar kasar Sin, yayin da Birtaniya ta janye jiki daga jefa kuri’a.

Labarai Masu Nasaba

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

Game da batun, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana a taron manema labaru yau Laraba cewa, Amurka ta sake yin fatali da daftarin kudurin kwamitin sulhu na MDD kan zirin Gaza, lamarin da ya sa al’ummar Gaza cikin wani yanayi mai hadari.

Da take karin haske kan wannan tambaya, Mao Ning ta yi nuni da cewa, halin da ake ciki na jin kai a Gaza, yana da matukar muni, kuma zaman lafiya da kwanciyar hankali na yankin ya yi tasiri sosai. Tilas ne kwamitin sulhun ya dauki matakai cikin gaggawa don inganta tsagaita bude wuta da kuma kawo karshen yakin.

Mao ta ce, kasar Sin za ta ci gaba da yin hadin gwiwa da dukkan bangarori na kasa da kasa, wajen ingiza kwamitin sulhu na MDD ya dauki matakan da suka dace, da yin kokarin kawo karshen yakin Gaza nan da nan, da sassauta yanayin jin kai, da sa kaimi ga aiwatar da shirin kafa kasashe biyu da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali na dogon lokaci a yankin Gabas ta Tsakiya. (Ibrahim Yaya, Safiyah Ma)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GazaIsra'ilawaMDDNATO
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabuwar Shugabar Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙasa.

Next Post

Mun Hana Kai Wa ‘Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba – Dauda

Related

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

1 hour ago
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

1 hour ago
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%
Daga Birnin Sin

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

2 hours ago
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

3 hours ago
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro
Daga Birnin Sin

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

4 hours ago
Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 
Daga Birnin Sin

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

23 hours ago
Next Post
Mun Hana Kai Wa ‘Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba – Dauda

Mun Hana Kai Wa 'Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba - Dauda

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

July 15, 2025
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

July 15, 2025
Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.