• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Tona Asirin Kungiyoyin Addinin Da Ke Daukar Nauyin Ta’addanci

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Sake Dawowar Matsalar Tsaro

A Nigerian military officer directs civilians at a checkpoint along Sapele-Warr road in the Niger Delta region May 26, 2009. Nigerian security forces repelled an attempted attack on an offshore oil drilling platform operated by French energy company Total on Tuesday, a security contractor working in the oil industry said. Around five attackers in a speedboat exchanged fire with security personnel shortly after dawn close to the platform at Total's 125,000 barrels per day Amenam field, located around 30 km (19 miles) from the coast of the Niger Delta. REUTERS/Afolabi Sotunde (NIGERIA CONFLICT ENERGY POLITICS BUSINESS CRIME LAW)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ikirarin shugabgan hukumar yaki ta cin hanci da rashawa, (EFCC), Ola Olukoyede, ya yi na cewa, akwai wasu manyan ‘yan Nijeriya ne ke daukar nauyin harkokin ‘yan ta’adda a Nijeriya ba wani sabon abu ba ne, ko ba komai bayanin ya tuna wa al’umma ne abin da suka dade suna ji daga bakin manyan ma’aikatan gwamnatin da suka gabata. Abin da ya bambanta a wannan ikirarin shi ne bayanin ya danganta manyan malaman addini da wannan aiki na daukar nauyin ta’addanci a Nijeriya.

Kwanaki ne shugaban hukumar EFCC, Olukoyede ya ce, hukumar ta gano wata kungiyar addini da ke yi wa ‘yan ta’adda safarar kudade da badda da masu da sawun kudadensu. Wannan ya zama wani sabon salo a kan takaddamar da take tattare da bayanan da ake yi a kan masu daukar nauyin ‘yan ta’adda a Nijeriya. Ya kuma kara da cewa, an gano wata kungiyar addini ta na boye wa ‘yan ta’addan kudade, bayan da aka bi diddigin wasu kudade daga ‘yan ta’addan zuwa asusun bankin kungiyar addinin.

  • Blinken: Idan Ba Ka Da Karfi, Za A Cinye Ka
  • Kasar Sin Za Ta Kafa Tsarin Ba Da Agajin Gaggawa Na Yau Da Kullum Don Inganta Sakamakon Kawar Da Kangin Talauci

“Mun bi diddigin kudaden zuwa asusun kungiyar addinin, da muka bayyana musu abin da muka gano a binciken mu sai muka samu umarni daga sama na mu dakatar da binciken,” in ji shi.

Amma kuma, bayan da rahottanin kafafen watsa labarai ya nuna cewa, bayanan shugaban EFCC na nuni ne ga wata coci, sai gashi sun fitar da wani rahoto mai ban dariya, inda suka ce ba suna nufin wata coci ko masallaci ba ne, amma sunan nufin kungiyar addini ne ko akida.

Sanarwar EFCC ta kuma ce, “Wadanda suke fassara bayanan shugaban EFCC na nuna cewa, yana nufin wata coci ke daukar nauyin ‘yan ta’adda, suna yi ne don cimma wata manufa tasu, wannan kuma ba zai taba kawar da shugaban EFCC daga aikin da ke gabansa ba na tsaftace kasar nan daga harkokin masu yi wa kasa zagon kasa.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

Ya kamata hukumar EFCC ta gane cewa, baya ga masu bautar addinin gargajiya da masu sauran addini daban daban akwai kuma manyan addinin kasar nan da suka hada da Kiristanity da addnin musulunci.

Rashin bayyana cikakken sunan coci ko masallacin da ke daukar nauyin harkokin ta’addanci, yanzu kusan makonni ke nan da yin haka, yana nuna lallai kamar hukumar EFCC ta fada dambarwar siyasa ke nan, musamman ganin yau makwanni ke nan da wannan bayanin amma har yau ba mu ji wani matakin da suka dauka ba na bankado kungiyar addnin da suke zargi da daukar nauyin masu aikata ta’addanci ba.

Saboda muhimmanci lamari irin wannan, ya kamata ‘yan Nijeriya su san halin da ake ciki kuma a cikin gaggawa. In har EFCC na so a dauki lamarinta da muhimmanci a nan gaba, dole a cikin gaggawa su sanar da ‘yan Nijeriya kungiyar addinin da ke safarar kudade ga kungiyoyin ‘yan ta’adda tare kuma da tabbatar da an gudanar da cikakken bincike da zai kai ga hukunta duk wanda ke da hannun a kan wannna danyen aikin.

A ‘yan shekarun nan, ‘yan ta’adda sun kashe ‘yan Nijeriya da dama da lalata dukiyoyin al’umma da dama da ba za su misaltu ba. duk da cewa, ba yaki ake yi ba, ayyukan ‘yan ta’adda na tayar da hankula, musamman ganin dimbin al’ummar da suka mutu da kuma wadanda aka raba da gidajensu ga kuma wadanda aka yi garkuwa da su, da kuma miliyoyin kudaden da aka biya da sunan diyya.

A kasar nan, musamman ganin irin tashin hankalin da ke tattare da ayyukan ‘yan ta’addan. Wannan bayani daga hukumar EFCC abu ne da ya kamata a dauka da matukar muhimmanci.

A matsayinmu na gidan jarida, hankalinmu a tashe yake ganin cewa, tun daga lokacin da shugabnan EFCC ya yi wannan bayanin, har yanzu ba a yi komai ba na karin bayani da kuma matakan da za su dauka a kan lamarin, musamman ganin muhimmancin lamarin, muna fatan wannan ma ba zai shude ba kamar yadda wasu lamura masu muhimmanci suke tafiya ba tare da an dauki mataki a kan su ba.

Dalilai da dama sun taikama wajen bunkasar harkokin ‘yan ta’adda a kasar, cikin su kuwa sun hada da rashin tsaro a iyakokin kasar nan, yawaitar makamai a cikin al’umma, talauci da kuma rashin aikin yi a taskanin matasa. Wani abu mai matukar muhimmanci kuma shi ne masu daukar nauyin ‘yan ta’addan, muna kuma kalubalantar jami’an tsaron su bayyana wa al’umma sunaye da adireshin masu daukar nauyin ta’addancin da nufin hukunta su ba tare da bata lokaci ba.

Idan za a iya tunawa gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ta sha yin magana a kan za ta bayyana sunayen masu daukar nauyin ‘yan ta’adda amma har ya sauka daga mulki bai yi haka ba kuma ba a kai ga hukunta kowa ba. Wannan kuma ya faru ne duk da muhimman bayanai da gwamnatin Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta ba gwamnatin na wadanda suke daukar nauyin ‘yan ta’adda.

A daidai wannan lokacin da kowa da kowa ke bukatar ganin an kawo karshen ta’addanci, dole a yanke kafafen samun kudaden ‘yan ta’adda tare da bayyana sunayen masu yi musu safarar kudaden, ta yadda za su kunyata a idon jama’a, kuma gaggauta gurfanar da su domin hukunta su. Saboda laifin su na daukar nauyin ta’addanci ya fi ayyukan ‘yan ta’addan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Fidda Gwani: Gwamna Dauda Ya Ayyana Ighodalo A Matsayin Ɗan Takardar PDP A Zaɓen Jihar Edo

Next Post

Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci

Related

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
Manyan Labarai

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

2 hours ago
ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

5 hours ago
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

5 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

6 hours ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Manyan Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

7 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

17 hours ago
Next Post
Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci

Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

July 8, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kuɓutar Da ‘Yan Ghana 19 Da Aka Yaudare Su Zuwa Nijeriya

July 8, 2025
ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

July 8, 2025
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

July 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

July 8, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.