• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Hada Hannu Da Maharba Wajan Samar Da Zaman Lafiya A Adamawa -Rundunar Soja ta 23

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Adamawa

A ci gaba da nuna goyon baya ga rundunar sojan Nijeriya wajen dakile aikata duk wani nau’in aikata miyagun ayyuka, kungiyar maharba da tsaron dazuka ta Kasa (NHFSS), reshen jihar Adamawa, ta bayyana bayar da guduwa ga rundunar soji ta 23 da ke Yola.

Malam Aminu Hammanjoda Furo, shugaban kungiyar ya bayyana haka ranar Juma’a, lokacin da ya ziyarci Kwamandan rundunar ta 23 da ke Yola, Birgediya Janar Paul Kefas Zawaya, a hedikwatar rundunar.

  • ‘Yan Bindiga: Gwamna Dauda Ya Kai Ziyarar Jaje A Zurmi Da Birnin Magaji
  • Kudurin Kirkiro ‘Yansandan Jihohi Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Zauren Majalisa

Furo ya ci gaba da cewa “an kafa kungiyar tsaron ne domin inganta zaman lafiya da tsaron al’ummar Adamawa, musamman a yankuna, lungu da sakon jihar.

“A shirye kungiyar mu take na bada goyon baya ga rundunar soji ta 23, ta hanyar bayanan tsaro akan lokaci wanda zai taimaka wajen daukan mataki akan lokaci, domin fatattakar ‘yan ta’addan da ke amfani da dazuzzuka a matsayin maboyarsu bayan sun aikata miyagun ayyuka” inji Furo.

Da yake maida kalami Kwamandan rundunar soji ta 23 da ke Yola, Birgediya Janar Paul Kefas Zawaya, ya yaba da ayyukan ‘yan kungiyar mafarautan, inda ya tabbatar da goyon rundunar soji ga kungiyar, “rundunar soji ta 23 ta himmatu wajen tuntubar juna don samar da hadinkai da daidaikun mutane, kungiyoyi domin isar da sakon zaman lafiya ga al’umma” inji Zawaya.

LABARAI MASU NASABA

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

Haka kuma shugaban rundunar soji ta 23 da ke Yola, ya yabawa gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, bisa kokarin ganin kungiyar mafarautan na aikin taimakawa jami’an tsaro, a yaki da duk nau’in miyagun laifuka a jihar.

Kwamandan rundunar sojin ya kuma bukaci ‘ya’yan kungiyar maharban da su kasance masu taka tsantsan da kwatanta adalci da kiyaye cin zarafin mutanen da ba su ji ba su gani ba lokacin gudanar da aiki

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 
Manyan Labarai

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
Manyan Labarai

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo
Manyan Labarai

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Next Post
Tsadar Rayuwa: Yadda Lamarin Ke Rincabe Wa Almajira Da Mabarata

Tsadar Rayuwa: Yadda Lamarin Ke Rincabe Wa Almajira Da Mabarata

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.