ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga: Gwamna Dauda Ya Kai Ziyarar Jaje A Zurmi Da Birnin Magaji

by Leadership Hausa
2 years ago
gwamna

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal a Juma’ar nan ya ziyarci al’ummomin Ƙananan Hukumomin Zurmi da Birnin Magaji bisa harin ta’addancin da ‘yan bindiga suka kai, inda Gwamnan ya jaddada aniyarsa ta kawo ƙarshen matsalar tsaron da jihar ke fama da shi.

In dai ba a manta ba, a makon da ya gabata ne ‘yan bindiga suka kai hare-hare a Nassarawar Zurmi da ke Ƙaramar Hukumar Zurmi da Nasarawar Godel da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Magaji a cikin jihar ta Zamfara.

A sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu a Gusau, ya bayyana cewa ziyarar ta kasance ta jaje ce da ta’aziyya ga al’ummar da wannan bala’i ya shafa na asarar rayuka, tare da nuna cewa gwamnati na tare da su.

ADVERTISEMENT

Ya ce, Gwamnan ya nuna wa jama’ar cewa yana tare da su, ya kuma tabbatar da jajircewar gwamnatinsa wajen lalubo sahihiyar hanyar kawo ƙarshen wannan bala’i da ya addabi jihar.

  • Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci

 

LABARAI MASU NASABA

Sirrin Mallakar Miji 

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Sanarwar ta Malam Idris ta kuma bayyana cewa, a yayin da Gwamna Dauda ya kai ziyarar gani da ido ga ofishin ‘yan sanda na Zurmi, wanda ‘yan ta’addan suka ƙona, ya nuna masu a shirye yake wajen samar masu da duk kayan aikin da suke nema don wannan namijin aiki.

Gwamna Lawal ya ce, “Ina miƙa saƙon ta’aziyya ta game da jami’ai biyu da suka rasa rayukansu a harin da ‘yan bindiga suka kai wa Nasarawar Zurmi. Ina sane da irin tashin hankalin da ke tattare da irin wannan bala’i ga duk wanda ta rutsa da shi, ina tabbatar maku, tare da iyalan waɗannan gwaraza, cewa ina tare da duk al’ummar wannan yanki a cikin addu’o’i na.

“Na yi matuƙar jinjina ga ƙoƙarin jajirtattun jami’an tsaronmu masu yaƙi da ta’addanci. Jajircewar ku na ganin kun kare al’ummar mu daga ‘yan ta’adda, wannan abin yabawa ne.

“Gwamnati na za ta ci gaba da bayar da duk wani taimako da dakarun muke buƙata. Tare za mu kawo ƙarshen waɗannan matsaloli, kuma mu ƙara ƙarfi.”

A lokacin da Gwamna Lawal ya shiga garin Zurmi, ya kai gaisuwar ban-girma ga Sarkin Zurmi, Alhaji Bello Sulaiman.

Da yake jawabi ga jama’ar Nasarawar Godal da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Magaji kuwa, Gwamna Lawal ya tabbatar masu da cewa ya riga ya aiko da kayan tallafi tun lokacin da abin ya faru.

“Na zo yau ne domin in nuna tausayawa ta da ta’aziyya ga iyalan waɗanda wannan abu ya shafa, tare da tabbatar da cewa gwamnati na ba za ta numfasa ba, har sai ta kawo ƙarshen wannan rashin tsaro.

“Ina fata wannan ziyara tawa za ta miƙa wani saƙon kyakkywar fata ga al’ummar Nasarawar, tare da tabbatar masu da cewa muna tare da su a wannan mawiyacin hali.

A lokacin da ya ke dawowa zuwa Gusau, Gwamna Lawal ya yada zango a Kasuwar Daji da ke Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda don jajanta wa Alhaji Hamisu Kasuwar Daji, wanda waɗannan ‘yan ta’adda suka kai wa gidansa hari.

gwamna
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Sirrin Mallakar Miji 
Adon Gari

Sirrin Mallakar Miji 

January 25, 2026
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Next Post
Nazari Kan Noman Citta A Zamanance

Nazari Kan Noman Citta A Zamanance

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.