ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga: Gwamna Dauda Ya Kai Ziyarar Jaje A Zurmi Da Birnin Magaji

by Leadership Hausa
3 years ago
gwamna

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal a Juma’ar nan ya ziyarci al’ummomin Ƙananan Hukumomin Zurmi da Birnin Magaji bisa harin ta’addancin da ‘yan bindiga suka kai, inda Gwamnan ya jaddada aniyarsa ta kawo ƙarshen matsalar tsaron da jihar ke fama da shi.

In dai ba a manta ba, a makon da ya gabata ne ‘yan bindiga suka kai hare-hare a Nassarawar Zurmi da ke Ƙaramar Hukumar Zurmi da Nasarawar Godel da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Magaji a cikin jihar ta Zamfara.

A sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu a Gusau, ya bayyana cewa ziyarar ta kasance ta jaje ce da ta’aziyya ga al’ummar da wannan bala’i ya shafa na asarar rayuka, tare da nuna cewa gwamnati na tare da su.

ADVERTISEMENT

Ya ce, Gwamnan ya nuna wa jama’ar cewa yana tare da su, ya kuma tabbatar da jajircewar gwamnatinsa wajen lalubo sahihiyar hanyar kawo ƙarshen wannan bala’i da ya addabi jihar.

  • Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci

 

LABARAI MASU NASABA

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

Sirrin Mallakar Miji 

Sanarwar ta Malam Idris ta kuma bayyana cewa, a yayin da Gwamna Dauda ya kai ziyarar gani da ido ga ofishin ‘yan sanda na Zurmi, wanda ‘yan ta’addan suka ƙona, ya nuna masu a shirye yake wajen samar masu da duk kayan aikin da suke nema don wannan namijin aiki.

Gwamna Lawal ya ce, “Ina miƙa saƙon ta’aziyya ta game da jami’ai biyu da suka rasa rayukansu a harin da ‘yan bindiga suka kai wa Nasarawar Zurmi. Ina sane da irin tashin hankalin da ke tattare da irin wannan bala’i ga duk wanda ta rutsa da shi, ina tabbatar maku, tare da iyalan waɗannan gwaraza, cewa ina tare da duk al’ummar wannan yanki a cikin addu’o’i na.

“Na yi matuƙar jinjina ga ƙoƙarin jajirtattun jami’an tsaronmu masu yaƙi da ta’addanci. Jajircewar ku na ganin kun kare al’ummar mu daga ‘yan ta’adda, wannan abin yabawa ne.

“Gwamnati na za ta ci gaba da bayar da duk wani taimako da dakarun muke buƙata. Tare za mu kawo ƙarshen waɗannan matsaloli, kuma mu ƙara ƙarfi.”

A lokacin da Gwamna Lawal ya shiga garin Zurmi, ya kai gaisuwar ban-girma ga Sarkin Zurmi, Alhaji Bello Sulaiman.

Da yake jawabi ga jama’ar Nasarawar Godal da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Magaji kuwa, Gwamna Lawal ya tabbatar masu da cewa ya riga ya aiko da kayan tallafi tun lokacin da abin ya faru.

“Na zo yau ne domin in nuna tausayawa ta da ta’aziyya ga iyalan waɗanda wannan abu ya shafa, tare da tabbatar da cewa gwamnati na ba za ta numfasa ba, har sai ta kawo ƙarshen wannan rashin tsaro.

“Ina fata wannan ziyara tawa za ta miƙa wani saƙon kyakkywar fata ga al’ummar Nasarawar, tare da tabbatar masu da cewa muna tare da su a wannan mawiyacin hali.

A lokacin da ya ke dawowa zuwa Gusau, Gwamna Lawal ya yada zango a Kasuwar Daji da ke Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda don jajanta wa Alhaji Hamisu Kasuwar Daji, wanda waɗannan ‘yan ta’adda suka kai wa gidansa hari.

gwamna
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

gwamna
Adon Gari

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

July 19, 2026
Sirrin Mallakar Miji 
Adon Gari

Sirrin Mallakar Miji 

January 25, 2026
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Next Post
Nazari Kan Noman Citta A Zamanance

Nazari Kan Noman Citta A Zamanance

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.