• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa: Sojoji Sun Ƙaryata Jita-jitar Shirin Yi Wa Shugaba Tinubu Juyin Mulki

by Muhammad
1 year ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Tsadar Rayuwa: Sojoji Sun Ƙaryata Jita-jitar Shirin Yi Wa Shugaba Tinubu Juyin Mulki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar sojan Nijeriya ta musanta rade-radin da ake yi mata cewa tana yunkurin yin juyin mulki ga zababbiyar gwamnatin shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu.

Rundunar ta bayyana wannan rade-radi a matsayin “labari na karya” wani rahoto da wata jaridar yanar gizo da ba (LEADERSHIP HAUSA) ba ta wallafa a ranar Lahadin da ta gabata, kan zargin yunkurin yin juyin mulki a Nijeriya a sakamakon halin matsi da takura da tabarbarewar tattalin arziki da kasar ke fuskanta yanzu haka.

  • NLC Na Zargin Gwamnatin Nijeriya Da Shirya Kai Wa ‘Ya’yanta Hari Yayin Zanga-zangar Yunwa
  • Tsadar Rayuwa: An Ci Gaba Da Gudanar Da Zanga-zanga A Ibadan

Idan dai za a iya tunawa, kwanaki, babban hafsan sojojin kasa na Nijeriya, Janar Christopher Musa, ya gargadi mutanen da ke kira da a yi juyin mulki a kan halin matsin tattalin arziki da kasar ke ciki, ya kuma ja kunne kan masu yadawa da su daina yada irin wannan kalaman.

An samu wata jaridar yanar gizo, ta rawaito wani rahoto cewa an sanya wa rundunar tsaron fadar shugaban kasa cikin shirin ko-ta-kwana, a sakamakon wani yunkuri da ba a saba gani ba, wanda ya sa ake zargin yunkurin juyin mulki ne a Nijeriya.

Ta ce ta samu labarin ne kawai a ranar Lahadin da ta gabata cewa, zargin ya sa gaggawar da ta hada da Kwamandan Rundunar Sojojin Shugaban Kasa, Kanar Adebisi Onasanya da Shugaba Tinubu da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

“An sanya Brigade na Shugaban Kasa a cikin shirin ko-ta-kwana bayan wani yunkuri da ba a saba gani ba ya haifar da zargin juyin mulki.

“A makon da ya gabata, Kanar Onasanya ya gana da shugaban kasa da shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin kasar sau biyu cikin sa’o’i 20.

“Sun kuma sanya wasu manyan runduna a karkashin kulawa saboda shirin zanga-zangar,” in ji wata majiyar fadar shugaban kasa ta yanar gizo.

Ita ma kungiyar kwadago a Nijeriya (NLC) na shirin gudanar da zanga-zanga ta kwanaki biyu a fadin kasar, wadda za a yi a ranakun 27 da 28 ga watan Fabrairu kan halin da tattalin arzikin kasar ke ciki a halin yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Juyin MulkiNijeriyaTinubuTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

NLC Na Zargin Gwamnatin Nijeriya Da Shirya Kai Wa ‘Ya’yanta Hari Yayin Zanga-zangar Yunwa

Next Post

Gobara Ta Ƙone Gidan Ƙaramar Ministar Birnin Tarayya Abuja, Mariya Bunkure

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

16 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Gobara Ta Ƙone Gidan Ƙaramar Ministar Birnin Tarayya Abuja, Mariya Bunkure

Gobara Ta Ƙone Gidan Ƙaramar Ministar Birnin Tarayya Abuja, Mariya Bunkure

LABARAI MASU NASABA

Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.