ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NLC Na Zargin Gwamnatin Nijeriya Da Shirya Kai Wa ‘Ya’yanta Hari Yayin Zanga-zangar Yunwa

by Muhammad
2 years ago
NLC

Wani labari da BBC Hausa ta wallafa a shafinta ya ce, Kungiyar Ƙwadado ta Nijeriya NLC, ta zargi gwamnatin ƙasar da kitsa kai wa ‘ya’yanta hari a lokacin zanga-zangar da ƙungiyar ta shirya gudanarwa a faɗin ƙasar a ranakun 27 da 28 ga watan da muke ciki.

Cikin wata sanarwar da ƙungiyar ta fitar mai ɗauke da sa hannun shugabanta na ƙasa, Comrade Joe Ajaero, NLC ta zargi gwamnatin ƙasar da shirya amfani da wata ƙungiyar farar hula mai suna ‘Nigeria Civil Society Forum’ (NCSF), wajen kai wa ‘ya’yanta hari a lokacin zanga-zangar lumanar da ta shirya gudanarwa.

  • Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tsunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango
  • NLC Na Neman A Biya Ma’aikata Naira Miliyan Ɗaya A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashi

”NCSF na ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da gwamnati ta ɗauki nauyinsu, kuma za ta yi amfani da su don kawo cikas ga zanga-zangar lumana da ‘ya’yan ƙungiyarmu suka shirya don nuna adawa da yunwar da ƙasarmu ke ciki”, in ji Comrade Ajaero.

ADVERTISEMENT

Ƙungiyar ta ce tana son gwamnati ta fahimci cewa zalunci kan ‘ya’yanta ba shi ne zai yi maganin halin matsin tattalin arziki da yunwa da ƙasar ke ciki ba.

”Kamar yadda gwamnati ta yi a Minna da wasu biranen ƙasar, inda ta riƙa harba hayaƙi mai sai ƙwalla da dukan mata tare da kulle su, kawai don sun nuna damuwarsu kan yunwar da ke damunsu. Bai kamata a ɗauki nauyin wasu don hana mutane bayyana abin da ke damunsu ba. Bai kamata a tarwatsa waɗanda ke kukan yunwa da alburushi ko hayaƙi mai sa ƙwalla ba”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Ƙungiyar ta kuma jaddada aniyarta na gudanar da zanga-zangar da ta shirya yi a faɗin ƙasar a ranakun da ta tsara yinsa.

”A don haka NLC da sauran ƙawayenta za mu gudanar da zanga-zangar da muka shirya yi don nuna adawarmu kan tsadar rayuwa da matsin tattalin arziki da rashin tsaro da ƙasarmu ke fuskanta”, in ji Ajaero.

”A matsayinmu na ‘yan ƙasa, muna da ‘yancin gudanar da zanga-zangar, kuma tarihi na nuna cewa a koyaushe zanga-zangarmu ta lumana ce, sai dai a inda gwamnati ta haddasa hargitsi”, in ji Ajaero.

A baya-bayan nan dai hukumomin ƙasar sun riƙa kira ga ƙungiyar kwadagon ta jingine zanga-zangar da ta shirya gudanarwa kan tsadar rayuwa a ƙasar.

Ko a makon da ya gabata ma hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta yi kira ga ƙungiyar NLCn ta dakatar da zanga-zangar saboda dalilai na tsaro.

Haka shi ma ministan shari’a na ƙasar Lateef Fagbemi, cikin wata wasiƙa da ya aike wa lauyan ƙungiyar kwadagon, Femi Falana, ya yi kira ga ƙungiyar ta jingine zanga-zangar da ta shirya yi a faɗin ƙasar.

To sai dai a cikin wasiƙar martani da lauyan ya aike wa ministan ya buƙace shi da samar da jami’an tsaron da za su bai wa ‘ya’yan ƙungiyar kariya a lokacin zanga-zangar lumanar.

NLC
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Tsadar Rayuwa: Sojoji Sun Ƙaryata Jita-jitar Shirin Yi Wa Shugaba Tinubu Juyin Mulki

Tsadar Rayuwa: Sojoji Sun Ƙaryata Jita-jitar Shirin Yi Wa Shugaba Tinubu Juyin Mulki

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.