• English
  • Business News
Tuesday, June 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Amince Da Ware Mutum Uku Kacal Su Dauki Rahotannin Gwamnan Kebbi Ba – ‘Yan Jarida

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Ba Mu Amince Da Ware Mutum Uku Kacal Su Dauki Rahotannin Gwamnan Kebbi Ba – ‘Yan Jarida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar

Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa

Kungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ), bangaren wakilan gidajen jaridun kasar nan da ke a Jihar Kebbi, sun yi watsi da zaben mambobinta guda uku kacal da za su rika daukar rahotannin Gwamna Nasir Idris a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.
Hakan na kunshe ne a wata takardar sanarwa da aka raba wa manema labarai da shugabancin kungiyar tasu ta jihar mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar Alhaji El-Yukub Usman da sakatarenta Ibrahim Bello a Birnin Kebbi.
  • Ana Kokarin Rantsar Da ‘Yan APC 16 A Majalisar Filato Ta Barauniyar Hanya – Gwamnatin Jihar
Wannan kin amincewa ya biyo bayan wani taron tattaunawa da aka yi a Birnin Kebbi ranar Talata tsakanin mukaddashin Babban sakataren gidan gwamnati, Alhaji Ibrahim Saraki;  mukaddashin Babban sakatare na hidindimun gwamna, Alhaji Sagir Mahe, da mai ba da shawara na musamman kan harkokin yada labarai ga Gwamna Nasir Idris, Malam Yahaya Sarki.
Sauran wadanda suka halarci taron tattaunawar sun hada da, Alhaji Aliyu Bandado, mai bai wa gwamna Idris shawara kan sabbin kafafen yada labarai kuma MC ga Gwamna, Alhaji Faruk Bello-Birnin Kebbi.
A ganawar tasu, sun cimma matsayar cewa gwamnan ya ba da umarnin cewa ba ya son ganin sama da mambobin ‘yan jarida uku da za su rika daukar labarun fadar gwamnatinsa.
Da yake mayar da martani kan wannan, Shugaban kungiyar, Alhaji El-Yakubu Usman-Dabai, ya bayyana wannan matakin a matsayin ‘mara amfani’ ga bangaren inganta ayyukan gwamnatin Kebbi, da kuma aikin jarida.
“A halin yanzu  muna da mambobi sama da 18, Kuma kowani wakili suna da salon daukar labari daban-daban na cikin gida, masu wakiltar kafafen yada labarai daban-daban a ciki da wajen Nijeriya, bai dace ba da rashin da’a a ba da dama ga mambobi uku kacal.
“Ka da jami’an gwamnati su manta da cewa, muna da wakilan talabijin da rediyo da jaridu da kafafen yada labarai na yanar gizo wadanda salon gidajensu ya bambanta da juna.
“Lokacin da kuka dauki jaridu don yin ayyukanku, kuna tauye wa sauran ‘yan jarida hakkinsu na tsarin mulki na sanar da al’ummar Kebbi game da ayyukan alheri da gwamnan yake yi.
“Muna da mutanen da ke zaune a wurare masu nisa da ke dogaro da rediyo da talabijin kawai don samun bayanai game da manufofin gwamnatinsu da shirye-shiryen gwamnatinsu a jihar,” in ji shi.
Usman-Dabai ya bukaci jami’an da abin ya shafa da su janye matakin da suka dauka, kasancewar ‘yan jarida abokan aikinsu ne.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan JaridaAikiFadar GwamnatiGwamnaKebbiNUJ
ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Cafke Motoci 21 Makare Da Abincin Da Aka Yi Fasa-kwauri Zuwa Kasashe Makwabta

Next Post

Bai Kamata Jama’a Su Tsorata Da Bullar Zazzabin Lassa A Adamawa Ba – Kwamishinan Lafiya

Related

Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar
Labarai

Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar

2 hours ago
Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa
Manyan Labarai

Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa

5 hours ago
Mutum 10 Sun Mutu Sakamakon Harbe-harbe A Makarantar Sakandire A Kasar Austriya
Manyan Labarai

Mutum 10 Sun Mutu Sakamakon Harbe-harbe A Makarantar Sakandire A Kasar Austriya

7 hours ago
Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka
Ra'ayi Riga

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

7 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Yi Hawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda Na Haramta Hawan Sallah A Kano
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Yi Hawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda Na Haramta Hawan Sallah A Kano

10 hours ago
Sojoji Sun Kashe Babban Kwamandan Boko Haram A Jihar Yobe
Labarai

Sojoji Sun Kashe Babban Kwamandan Boko Haram A Jihar Yobe

11 hours ago
Next Post
Bai Kamata Jama’a Su Tsorata Da Bullar Zazzabin Lassa A Adamawa Ba – Kwamishinan Lafiya

Bai Kamata Jama'a Su Tsorata Da Bullar Zazzabin Lassa A Adamawa Ba - Kwamishinan Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Ya Gabatar Da Jawabi Albarkacin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” Karo Na Farko Na MDD

Wang Yi Ya Gabatar Da Jawabi Albarkacin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” Karo Na Farko Na MDD

June 10, 2025
Sin Da Kenya Sun Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Kiwon Lafiya

Sin Da Kenya Sun Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Kiwon Lafiya

June 10, 2025
Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar

Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar

June 10, 2025
Xi Ya Zanta Da Takwaransa Na Kasar Koriya Ta Kudu  

Xi Ya Zanta Da Takwaransa Na Kasar Koriya Ta Kudu  

June 10, 2025
Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu

Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu

June 10, 2025
Sin Na Maraba Da Karin ‘Yan Kasuwar Ketare Dake Son Gudanar Da Hada-hada Don Cimma Moriyar Juna

Sin Na Maraba Da Karin ‘Yan Kasuwar Ketare Dake Son Gudanar Da Hada-hada Don Cimma Moriyar Juna

June 10, 2025
Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa

Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa

June 10, 2025
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Babban Taron MDD Kan Tekuna

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Babban Taron MDD Kan Tekuna

June 10, 2025
Mutum 10 Sun Mutu Sakamakon Harbe-harbe A Makarantar Sakandire A Kasar Austriya

Mutum 10 Sun Mutu Sakamakon Harbe-harbe A Makarantar Sakandire A Kasar Austriya

June 10, 2025
Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

June 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.