• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kebbi Ya Raba Motoci 24 ga ‘Yan Majalisar Jihar

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Kebbi Ya Raba Motoci 24 ga ‘Yan Majalisar Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris ya raba sabbin motoci kirar Toyota Fortuner Jeep guda 24 ga ‘yan majalisar dokokin jihar, domin kara karfafa musu gwiwa wajen gudanar da ayyukansu.

Gwamnan wanda ya mika motocin ga kakakin majalisar Hon. Muhammad Usman Ankwai tare da wasu ’yan majalisa a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi, ya bukace su da su yi amfani da motocin ta hanyar da ya kamata.

  • Dubai Ba Ta Dage Haramcin Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza Ba – Fadar Shugaban Kasa
  • Yadda Aka Fara Zaben Fidda Gwani A Amurka

Ya kuma lura cewa motocin za su taimaka matuka wajen taimaka wa ‘yan majalisar wajen gudanar da ayyukansu na majalisa da himma domin ci gaban jihar.

Ya yaba da kyakkyawar alakar aiki da ke tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa, wanda a cewarsa, ya samar da hanyar gudanar da ayyukan raya jihar daban-daban cikin sauki, wadanda ke da alaka kai tsaye ga rayuwar jama’a.

Gwamna Idris ya karfafa gwiwar ‘yan majalisar da su dore da kyakkyawar alakar da ke tsakaninta da jihar domin samun ci gaba cikin sauri da ciyar da jihar a gaba.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

“Dole ne na bayyana a nan cewa ina jin dadin zaman lafiya da ke tsakaninmu, ban taba samun sabani da shugaban majalisar ko da mambobinsa ba.

“Wannan, a zahiri ya taimaka mana wajen aiwatar da ayyuka a duk masarautunmu na gargajiya da muke da a fadin jihar don amfanin mutanenmu,” in ji shi.

Gwamnan ya tuna cewa ya saya tare da raba sabbin motoci guda 30 ga jami’an tsaro, 28 ga kwamishinoni da wasu shugabannin hukumomin.

Ya ce: “A yau muna shaidar rabon sabbin motoci kirar Toyoa Fortuner Jeep guda 24 ga ‘yan majalisar dokokin Jihar Kebbi.

Ya ce gwamnatinsa ta zabi sabbin motoci ne domin kaucewa duk wata gazawa wajen gudanar da ayyukansu.

Daga nan sai ya bukaci wadanda suka ci gajiyar motocin da su yi amfani da ababen hawan domin cimma manufar da aka nufa da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Edo Na Shirin Tsige Mataimakin Gwamnan Jihar

Next Post

Ma’aikatan Shari’a Sun Janye Yajin Aiki A Osun

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

4 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

5 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

6 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

11 hours ago
Kebbi
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

11 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

12 hours ago
Next Post
Ma’aikatan Shari’a Sun Janye Yajin Aiki A Osun

Ma'aikatan Shari'a Sun Janye Yajin Aiki A Osun

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.