• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan CBN Ya Gargadi Nijeriya Kan Hatsarin Laftan Basuka

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan CBN Ya Gargadi Nijeriya Kan Hatsarin Laftan Basuka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Olayemi Cardoso, ya gargadi Nijeriya da sauran kasashe masu tasowa da su yi taka-tsan-tsan kan hadarin bashi, yana mai cewa idan ba a magance su ba za su kawo cikas ga ci gaba n tattalin arziki da wadata.

Gwamnan CBN ya kuma ce a halin da Nijeriya ke ciki na gaf da shiga hatsarin basuka, duba da halin da kasuwan duniya ke ciki da kuma karuwar basuka da ya samu asali tun daga barkewar cutar Korona.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kara Gina Madatsun Ruwa Domin Noman Rani

Masana da dama dai sun jima suna yekuwar cewa tulin basukan da Nijeriya ke kai ne suka zama asasin matsalolin tattalin arziki da ke kara haifar da matsaloli a kasar nan musamman na matsin rayuwa.

Duk da basuka masu yawa da ake bin Nijeriya na ciki da waje, har yanzu jagororin kasar a matakin tarayya da jihohi na ci gaba da kinkimo wa kansu basuka.

Lamarin da ke kara maida al’umman kasar cikin mummunn talauci da fatara, musamman tun bayan cire tallafin man fetur a farkon hawan wannan gwamnatin da kuma karyewar darajar naira.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Sai dai Cardoso ya ce, hatsarin da babban bankin duniya da asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) suka bayyana, na nuni da cewa Nijeriya na fuskantar barazana.

Ya shaida hakan ne a Abuja lokacin kaddamar da taron masu ruwa da tsaki kan basuka na bankin duniya, IMF, (WAIFEM).

Ya samu wakilcin daraktan tsare-tsaren kudade, Dakta Mohammed Musa Tumala, ya ce, “Domin tabbatar da harkokin ciyo basuka na gudana bisa matakin da suka dace, kauce wa fadawa cikin hatsari da kuma shawo kansu.”

Ya ce, dole ne ya zama duk wani bashin da za a ciyo a yi nazari kuma a tabbatar an bi matakan ciyo bashi domin tabbatar da kiyaye matsalolin da ka iya janyowa a nan gaba.

Ana bin jihohi da gwamnatin tarayya basukan da suka kai naira tiriliyan 139, a rahotonnin da suke akwai.

A jawabinsa tun da farko, daraktan cibiyar hada-hadar kudade da tattalin arziki na Yammacin Afrika, (WAIFEM), Dakt Baba Y. Musa, ya shawarci gwamnatin tarayya da ta maida hankali kan barazanar kara tara wa kanta basuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikita-rikitar Sauka Da Komawar Sheikh Daurawa Shugabancin Hisbar Jihar Kano

Next Post

Ba Za Mu Lamunci Cin Zarafin Wani Da Sunan Tafsiri Ba – Gwamnatin Kaduna

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

7 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

8 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

11 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

13 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

16 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

17 hours ago
Next Post
Uba sani

Ba Za Mu Lamunci Cin Zarafin Wani Da Sunan Tafsiri Ba - Gwamnatin Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.