• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan CBN Ya Gargadi Nijeriya Kan Hatsarin Laftan Basuka

by Khalid Idris Doya
2 years ago
CBN

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Olayemi Cardoso, ya gargadi Nijeriya da sauran kasashe masu tasowa da su yi taka-tsan-tsan kan hadarin bashi, yana mai cewa idan ba a magance su ba za su kawo cikas ga ci gaba n tattalin arziki da wadata.

Gwamnan CBN ya kuma ce a halin da Nijeriya ke ciki na gaf da shiga hatsarin basuka, duba da halin da kasuwan duniya ke ciki da kuma karuwar basuka da ya samu asali tun daga barkewar cutar Korona.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kara Gina Madatsun Ruwa Domin Noman Rani

Masana da dama dai sun jima suna yekuwar cewa tulin basukan da Nijeriya ke kai ne suka zama asasin matsalolin tattalin arziki da ke kara haifar da matsaloli a kasar nan musamman na matsin rayuwa.

Duk da basuka masu yawa da ake bin Nijeriya na ciki da waje, har yanzu jagororin kasar a matakin tarayya da jihohi na ci gaba da kinkimo wa kansu basuka.

Lamarin da ke kara maida al’umman kasar cikin mummunn talauci da fatara, musamman tun bayan cire tallafin man fetur a farkon hawan wannan gwamnatin da kuma karyewar darajar naira.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Sai dai Cardoso ya ce, hatsarin da babban bankin duniya da asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) suka bayyana, na nuni da cewa Nijeriya na fuskantar barazana.

Ya shaida hakan ne a Abuja lokacin kaddamar da taron masu ruwa da tsaki kan basuka na bankin duniya, IMF, (WAIFEM).

Ya samu wakilcin daraktan tsare-tsaren kudade, Dakta Mohammed Musa Tumala, ya ce, “Domin tabbatar da harkokin ciyo basuka na gudana bisa matakin da suka dace, kauce wa fadawa cikin hatsari da kuma shawo kansu.”

Ya ce, dole ne ya zama duk wani bashin da za a ciyo a yi nazari kuma a tabbatar an bi matakan ciyo bashi domin tabbatar da kiyaye matsalolin da ka iya janyowa a nan gaba.

Ana bin jihohi da gwamnatin tarayya basukan da suka kai naira tiriliyan 139, a rahotonnin da suke akwai.

A jawabinsa tun da farko, daraktan cibiyar hada-hadar kudade da tattalin arziki na Yammacin Afrika, (WAIFEM), Dakt Baba Y. Musa, ya shawarci gwamnatin tarayya da ta maida hankali kan barazanar kara tara wa kanta basuka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
Uba sani

Ba Za Mu Lamunci Cin Zarafin Wani Da Sunan Tafsiri Ba - Gwamnatin Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.