ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
Tarayya

Gwamnatin tarayya ta amince da gina sabbin gidaje ga shugabannin manyan kotuna da kuma aiwatar da muhimman ayyukan ruwa da ci gaban tituna a babban birnin tarayya (FCT). Ministan FCT, Nyesom Wike, ne ya bayyana hakan ga manema labarai bayan taron majalisar zartarwa ta tarayya (FEC) da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta a ranar Alhamis.

Wike ya bayyana cewa sabbin gidajen za a gina su ne domin Shugaban Kotun ɗaukaka ƙara (Court of Appeal), Shugaban Kotun Ma’aikata ta Ƙasa (National Industrial Court), da babban alƙalin Kotun Tarayya (Federal High Court), da kuma babban alƙalin kotun FCT (FCT High Court). Ya ce wannan mataki na cikin ƙoƙarin gwamnati na samar da muhallin da ya dace ga manyan jami’an shari’a domin sauƙaƙa aiyukansu.

  • Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 
  • Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

A ɓangaren aiyukan ruwa, Wike ya bayyana cewa majalisar ta amince da aikin samar da ruwan sha ga yankunan Karu, da Karshi, da Orozo da Bwari, wanda ya kasance ci gaban shirin samar da ruwa na birnin tarayya (Greater Abuja Water Supply Project). Ya ce tuni an fara kuma ana sa ran kammala shi kafin watan Mayu na shekara mai zuwa. “Shugaban ƙasa ya sha alwashin cewa ruwan Abuja zai isa ƙananan yankuna, kuma mun riga mun ƙaddamar da wannan aiki,” in ji Wike.

ADVERTISEMENT

Ministan ya kuma bayyana cewa FEC ta amince da aiwatar da gyaran gaggawa da aka yi wa babban ɗakin taro na Bola Ahmed Tinubu )International Conference Centre), wanda aka sabunta domin taron majalisar ECOWAS da aka gudanar a baya. Ya ce aikin ya kammala cikin lokaci kuma an buɗe shi bayan tabbatar da cewa ya kai matsayin ƙasa da ƙasa.

Haka zalika, Wike ya bayyana cewa FEC ta amince da sabunta ƙwangilar samar da gine gine a sabon yankin Maitama 2, wanda ya mamaye fili sama da hekta 786. Ya ce aikin ya tsaya tun shekaru biyar da suka wuce, amma yanzu an sake farfaɗo da shi domin bunƙasa sabon yankin birnin. “Wannan yana daga cikin manyan ayyukan babban birnin tarayya ake aiwatarwa, kuma gwamnati za ta tabbatar da an kammala shi cikin nasara,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Guguwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutum Huɗu, Ta Yi Mummunar Ɓarna A Sokoto

Badaƙalar Binciken Hukumar Bogi: Gbajabiamila Ya Gurfana Gaban ICPC

Tarayya
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir
  • Abubakar Sulaiman
    Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi
  • Abubakar Sulaiman
    Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu
  • Abubakar Sulaiman
    ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya

MASU ALAKA

nema
Manyan Labarai

Guguwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutum Huɗu, Ta Yi Mummunar Ɓarna A Sokoto

July 21, 2026
ICPC
Manyan Labarai

Badaƙalar Binciken Hukumar Bogi: Gbajabiamila Ya Gurfana Gaban ICPC

July 21, 2026
Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu
Manyan Labarai

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

July 20, 2026
Next Post
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi

July 21, 2026
Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina

Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina

July 21, 2026
nema

Guguwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutum Huɗu, Ta Yi Mummunar Ɓarna A Sokoto

July 21, 2026
Hadarin Kwale-Kwale

Mutum Ɗaya Ya Mutu, Sama Da 30 Sun Ɓace A Hatsarin Kwale-kwale A Jigawa

July 21, 2026
ICPC

Badaƙalar Binciken Hukumar Bogi: Gbajabiamila Ya Gurfana Gaban ICPC

July 21, 2026
Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

July 20, 2026
Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

July 20, 2026
Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

July 20, 2026
NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

July 20, 2026
Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

July 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.