• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Lauyoyi Ta Tabbatar Da Fara Gurfanar Da Masu Laifukan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Kungiyar Lauyoyi Ta Tabbatar Da Fara Gurfanar Da Masu Laifukan Zaben 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya karkashin kungiyar lauyoyi ta Nijeriya (NBA) ta fara gurfanar da wasu jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da mambobin jam’iyyar siyasa bisa samun su da laifuka daban-daban a lokacin gudanar da zaben 2023.   

Laifukan zabe sun kasance babban barazana ga gudanar da sahihin zabe a Nijeriya, domin sukan janyo tsananin gabar siyasa da kuma haddasa rikice-rikice.

  • Rikita-rikitar Sauka Da Komawar Sheikh Daurawa Shugabancin Hisbar Jihar Kano
  • Firaministan Kasar Malaysia Ya Ce Bai Kamata Ba A Yi Tsoron Bunkasuwar Kasar Sin

Bayan zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisu da ya gudana a ranar 25 ga Fabrairun 2023, rundunar ‘yansandar Nijeriya ta ce ta samu nasarar damke mutane sama da 700, bisa karya dokokin zabe.

A ranar 2 ga Mayun 2023, INEC ta ce ta gurfanar da mutum 215 cikin mutum 774 da ‘yansanda suka kama bisa aikata laifuka daban-daban da suka shafi zabe.

Hukumar INEC ta ce ta hada kai da kungiyar lauyoyin Nijeriya domin gurfanar da wadanda aka kama bisa karya dokokin zabe a gaban kuliya.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Daga cikin shari’o’i 215 da hukumar INEC ta samu, shari’o’i’ 196 sun kasance laifuka ne na karya dokokin zabe, wanda kuma INEC da lauyoyi suke kulawa da su.

Sakataren yada labarai na NBA, Habeeb Lawal, an gurfanar da wadanda ake zargi mutum 196 ciki har da jami’an INEC da mambobin jam’iyyun siyasa, bisa karya dokokin zabe da suka hada da sayan kuri’u, mallakar makamai da sauran laifuka da suka aikata lokacin zaben 2023.

Lawal ya kara da cewa an gurfanar da wadanda ake zargin ne a kotunan majestiri da sauran manyan kotuna da ke jihohi da kuma Abuja.

Ya ce, “An gurfanar da mutum 196 da ake zargi da karya dokokin zabe, kuma mambobin kungiyar lauyoyi ne ke kula da lamarin.

“Laifukan sun hada da sakaci wurin gudanar da aiki, kada kai wajen aikata ta’addanci, kawo hagitsi a wurin zabe, fito da makami lokacin zabe, satar akwatin zabe, lalata kayayyakin zabe, yin magudin zabe, mallakar kayayyakin zabe ba bisa ka’ida ba, rashin mayar da hankali lokacin zabe, sayar kuri’a da kuma kawo rikice-rikice a lokacin zabe.

“Wasu daga cikin wadanda ake zargin jami’an INEC ne, yayin da wasu mambobin jam’iyyun siyasa ne, sannan kuma wasu kuma ba su da alaka da harkokin siyasa.

“Kotunan majestiri da ke jihohi da Abuja suke kulawa da shari’o’in da suka danganci laifukan zabe kamar yadda dokar zabe ta tanada.

“Domin haka, mambobin kungiyarmu suna kulawa da wadannan shari’o’i a dukkan fadin kasar nan,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Garin Mada

Next Post

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Tallafawa Matakan Siyasa A Sudan

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

1 day ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 week ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

4 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

4 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

4 weeks ago
Next Post
Sudan

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Tallafawa Matakan Siyasa A Sudan

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.