ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Lauyoyi Ta Tabbatar Da Fara Gurfanar Da Masu Laifukan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Kungiyar Lauyoyi

Gwamnatin tarayya karkashin kungiyar lauyoyi ta Nijeriya (NBA) ta fara gurfanar da wasu jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da mambobin jam’iyyar siyasa bisa samun su da laifuka daban-daban a lokacin gudanar da zaben 2023.   

Laifukan zabe sun kasance babban barazana ga gudanar da sahihin zabe a Nijeriya, domin sukan janyo tsananin gabar siyasa da kuma haddasa rikice-rikice.

  • Rikita-rikitar Sauka Da Komawar Sheikh Daurawa Shugabancin Hisbar Jihar Kano
  • Firaministan Kasar Malaysia Ya Ce Bai Kamata Ba A Yi Tsoron Bunkasuwar Kasar Sin

Bayan zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisu da ya gudana a ranar 25 ga Fabrairun 2023, rundunar ‘yansandar Nijeriya ta ce ta samu nasarar damke mutane sama da 700, bisa karya dokokin zabe.

ADVERTISEMENT

A ranar 2 ga Mayun 2023, INEC ta ce ta gurfanar da mutum 215 cikin mutum 774 da ‘yansanda suka kama bisa aikata laifuka daban-daban da suka shafi zabe.

Hukumar INEC ta ce ta hada kai da kungiyar lauyoyin Nijeriya domin gurfanar da wadanda aka kama bisa karya dokokin zabe a gaban kuliya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Daga cikin shari’o’i 215 da hukumar INEC ta samu, shari’o’i’ 196 sun kasance laifuka ne na karya dokokin zabe, wanda kuma INEC da lauyoyi suke kulawa da su.

Sakataren yada labarai na NBA, Habeeb Lawal, an gurfanar da wadanda ake zargi mutum 196 ciki har da jami’an INEC da mambobin jam’iyyun siyasa, bisa karya dokokin zabe da suka hada da sayan kuri’u, mallakar makamai da sauran laifuka da suka aikata lokacin zaben 2023.

Lawal ya kara da cewa an gurfanar da wadanda ake zargin ne a kotunan majestiri da sauran manyan kotuna da ke jihohi da kuma Abuja.

Ya ce, “An gurfanar da mutum 196 da ake zargi da karya dokokin zabe, kuma mambobin kungiyar lauyoyi ne ke kula da lamarin.

“Laifukan sun hada da sakaci wurin gudanar da aiki, kada kai wajen aikata ta’addanci, kawo hagitsi a wurin zabe, fito da makami lokacin zabe, satar akwatin zabe, lalata kayayyakin zabe, yin magudin zabe, mallakar kayayyakin zabe ba bisa ka’ida ba, rashin mayar da hankali lokacin zabe, sayar kuri’a da kuma kawo rikice-rikice a lokacin zabe.

“Wasu daga cikin wadanda ake zargin jami’an INEC ne, yayin da wasu mambobin jam’iyyun siyasa ne, sannan kuma wasu kuma ba su da alaka da harkokin siyasa.

“Kotunan majestiri da ke jihohi da Abuja suke kulawa da shari’o’in da suka danganci laifukan zabe kamar yadda dokar zabe ta tanada.

“Domin haka, mambobin kungiyarmu suna kulawa da wadannan shari’o’i a dukkan fadin kasar nan,” in ji shi.

Kungiyar Lauyoyi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Sudan

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Tallafawa Matakan Siyasa A Sudan

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.