ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikita-rikitar Sauka Da Komawar Sheikh Daurawa Shugabancin Hisbar Jihar Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
Daurawa

Hukumar Hisba, hukuma ce da ke da hurumi a Shari’ar Musulunci, kasancewar babban aikinta shi ne umarni da aikin alhairi da kuma hani da mummunan aiki, an kaddamar Hukumar Hisba tun lokacin zangon farko na Gwamna Kwankwaso, amma ta samu cikakken gindin zama a shekara ta 2007 zamanin Mulkin Malam Ibrahim Shekaru inda Shugaban Hukumar Hisba na farko shi ne Sheikh Malam Yahaya Farouk Chedi bayan shi Kuma Malam Ibrahimahim Mai bushira.

Hukumar Hisba a Jihar Kano ba yanzu shugabaninta suka fara gamuwa da tunzuri daga wasu mutane da ke ganin aikin na Hisba na yin katsalandan ga sana’unsu ko ra’ayinsu, Malam Abdulkarin Abubakar Rabo wanda har wata wakar cin zarafi taron wasu mawaka suka yi masa saboda kawai ya matsa lamba kan daidaita sahun wasu rukunin al’umma da ake ganin suna kokarin gurbata tarbiyyar yara musamman mata.

  • Kano Za Ta Haɗa Gwiwa Da Afrinvest Don Haɓɓaka Kasuwanci Da Ci Gaban Jihar 
  • Yadda Sheikh Daurawa Ya Koma Ofis Bayan Sulhu Da Gwamnan Kano

Bayan samun sauyin Gwamnati ne kuma Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya sake darewa an karagar mulkin Kano kuma ya nada sabon Shugaban Hukumar ta Hisba Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, wanda kowa ya san shi mai goyon bayan Darikar Kwankwasiyya ne, sannan kowa ya san Daurawa a matsayin wanda ya samar da gagarumin ci gaba a harkokin gudanarwa hukumar, ciki har da nasarar bijiro da shirin auren zawarawa wanda ya dauki hankalin duniya baki daya.

ADVERTISEMENT

Halin da ake abin ya zama sahun gaba cikin abubuwan da dake daukar hankali a Kano bai wuce batun murabus din Daurawa ba, sakamakon jawabin da Gwamnan ya gabatar a lokacin taron daukacin mala-man addini da limamai da ya gudana a fadar Gwamnatin Kano, inda Gwamnan ya bayyana matakn Hukumar Hisba na yaki da badala da cewa bai ji dadin abin da ya gani a wani faifan bidiyo dake nuna ana dukkan matasa da gorori tare da rungumar mata ana jefa su cikin motar Jami’an Hisba.

Jin wannan kalamai na Gwamna na Kano ne ya sa Sheikh Daurawa bayyyana murabus daga mukaminsa na babban Kwamandan Hisba, inda ya bai wa gwamna hakuri tare da rokon afuwarsa, sannan ya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Lamarin da ake alakanta shi da fitsararriyar ‘yar TikTok Murja Kunya wadda ta shahara ta fuskar fitsara batsa da Kuma yadda wasu mazauna Unguwar Hotoro Suka yi kararta sakamakon yunkurin bata tarbiy-yar yaransu, hakan ta sa aka shelanta farautarta, wanda kuma jami’an na Hisba suka samu nasarar damke ta tare da gurfanar da ita gaban kuliya, inda daga nan alkalin kotun ya aika da ita gidan gyaran hali har zuwa lokacin da za’a dawo da ita kotu.

Amma wani abu mai kama da al’amara kawai sai aka wayi gari da jin labarin fitar da ita ba kuma tare da sanin alkalin da ya aikata Gidan Gyaran Halin ba.

Bayyana murabus din Daurawa ne ya sanya Limaman masallatan Juma’a Suka gabatar mafi yawan Hud-ubarsu kan wannan matsàla. Sai dai wasu Malamai na ta rokon Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa da dubi girman Allah ya koma bakin aikinsa. A washe garin murabus din na Daurawa wata majiyar ta Shaida wa Jaridar LEADERSHIP Hausa cewa an kwashe awa bakwai na gudanar taro kan lamarin

Babu shakka kalaman na Gwamnan Abba Kabir Yusuf ya zama abin da ko ina a Kano ke zaman abin tattaunawa, wasu na ganin barin tantiriyar ci gaba da wannan mummunar ta’adar zai kara zubarwa da Jihar Kano kimar da aka Santa dashi

Sheikh Daurawa Ya Amince Da Komawa Kan Mukaminsa

Sakamakon wani zama na musamman da wasu Malamai suka yi da Gwamnan Jihar Kano, an samu sasanci, yanzu Shaikh Aminu Daurawa zai ci gaba da shugabancin Hukumar Hisba a Kano,

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Litinin, ya bayyana cewa akwai wani zama da ya gudana tsakanin Gwamna Abba Kabir Yusuf da wata tawagar Malamai, wadanda suka hada da shi kan sa Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa bisa jago-rancin Dakta Musa Borodo da sauran Malamai irin su, Dakta Sa’idu Ahmad Dukawa, Sheikh Abdul-wahab Abdallah, Farfesa Salisu da sai sauransu.

A ta bangaren Gwamnati kuma, bisa jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, akwai mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano, Alhaji Jibrin Ismail Fal-gore; Sakataren Gwamnatin Jihar Kano Dakta Baffa Abdullahi Bichi, da Shugaban Ma’aikatan gidan Gwamnatin jihar, Alhaji Shehu Wada Sagagi.

Yanzu dai abin da yage shi ne sauraron jin irin salon da Kwamanda Hisbar Aminu Daurawa zai shigo da shi, shin ya gindaya wani sharadi ne kan daina yi wa ayyukan hukumar katsalandan da kokarin daurewa masu badala gindi, ko kuma an yi masa iyaka kan ayyukan na Hisba, wannan dai ta Bahaushe “Maji ma-gani, an binne tsohuwa da rai.

Daurawa
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Next Post
Gwamnan CBN Ya Gargadi Nijeriya Kan Hatsarin Laftan Basuka

Gwamnan CBN Ya Gargadi Nijeriya Kan Hatsarin Laftan Basuka

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.