• English
  • Business News
Saturday, August 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Dakatar Da Kociyan Mata Na Leicester City Kan Zargin Yin Soyayya Da ‘Yar Wasa

by Muhammad
1 year ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Wasanni
0
An Dakatar Da Kociyan Mata Na Leicester City Kan Zargin Yin Soyayya Da ‘Yar Wasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar ƙwallon ƙafar mata ta Leicester City ta fara bincike kan manajan tawagar Willie Kirk, game da zargin yana soyayya da wata daga cikin ‘yan wasansa.

TRT Afrika Hausa ta  ce, Jaridar The Guardian ta ruwaito cewa Leicester ta dakatar da manajan sakamakon zargin, yayin da take gudanar da bincike kan batun. Don haka ba zai jagoranci tawagar a wasansu na Asabar ɗin nan ba.

  • Birmingham City Ta Kori Rooney A Matsayin Kocinta
  • Kocin Super Eagles Jose Peseiro Ya Ajiye Aikinsa Bayan Karewar Kwantiraginsa

Ƙungiyar ta fitar da sanarwa mai cewa “Willie Kirk yana taimaka wa kulob ɗin wajen gudanar da binciken na cikin gida, inda za a fito da sakamakon bincike a gaba”.

Sanarwar ta ƙara da cewa a yanzu mataimakiyar manajan ƙungiyar, Jennifer Foster da kuma mai horar da tawagar Stephen Kirby, za su ɗauki ragamar ƙungiyar a wasansu na yau da za su kara da ƙungiyar Liverpool ta mata.

Shi dai kocin da aka dakatar, Willie Kirk ya karɓi ragamar Leicester ne tun watan Yuli na 2022, lokacin da aka naɗa shi daraktan wasanni na ƙungiyar.

Labarai Masu Nasaba

An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

Daga bisani ya zama manajan ƙungiyar ranar 3 ga watan Nuwamba, inda ya maye gurbin Lydia Bedford.

A baya ma, Kirk ya taɓa jagorantar ƙungiyar Hibernian Women ta mata, da Preston ta maza, da kuma Bristol City, da ma Everton, kafin ya koma Leicester.

Haka nan kuma, ya taɓa zama mataimakin kocin Manchester United na ɗan lokaci a shekarar 2018.

A yanzu dai Leicester tana mataki na bakwai a teburin Women Super League ta Ingila, da maki 16 bayan wasanni 15. Kuma a yau za ta fuskanci Liverpool da ke mataki na biyar a gasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DakatarwaKochiyaLeicester CitySoyayya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ramadan: Gwamnatin Katsina Ta Karya Farashin Kayan Abinci

Next Post

Mahaifin Matar Gwamnan Neja, Sarkin Malami Nupe Ya Rasu Yana Da Shekaru 90

Related

An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons
Wasanni

An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons

14 hours ago
Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna
Wasanni

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

4 days ago
Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig
Wasanni

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

7 days ago
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham
Wasanni

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

7 days ago
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace
Wasanni

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

7 days ago
UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari
Wasanni

UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

1 week ago
Next Post
Mahaifin Matar Gwamnan Neja, Sarkin Malami Nupe Ya Rasu Yana Da Shekaru 90

Mahaifin Matar Gwamnan Neja, Sarkin Malami Nupe Ya Rasu Yana Da Shekaru 90

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

August 15, 2025
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

August 15, 2025
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

August 15, 2025
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

August 15, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

August 15, 2025
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.