Hukumar zabe ta kasa INEC ta mayar da martani kan wani faifan bidiyon da ke yawo a kafafen sada zumunta da ya nuna ana birne katukan zabe a cikin magudanar ruwa a jihar Ribas.
A cewar hukumar, ana zargin cewa a gidan wani babban dan siyasa ne a jihar aka bankado katukan na jefa kuri’a.
- Zaben Osun: Yadda Mawaki Portable Ya Sha Suka Kan Goyon Bayan APC
- IPOB Ta Yi Barazana Ga Jakadiyar Birtaniya A Nijeriya
Sai dai, a rahotannin farko, katukan na zaben an bankado su ne a jihar Imo, inda a martanin da kwamishina kuma shugaban wayar da kan masu jefa kuri’a da ilimantar da su na INEC, Festus Okoye, ya yi ya bayyana cewa, a binciken farko da aka yi kan maganar ya nuna cewa, an bankado katukan ne a jihar Ribas ,
Okoye wanda ya sanar da hakan a wata hira da gidan talabijin na Arise da ke Abuja, a yau Juma’a’.
“Kalubalen da muka fuskanta da farko shi ne na kasa gano inda abin ya auku, inda ya kara da cewa, wasu sun ce ya auku ne a jihar Imo wasu kuma sun ce, ya auku ne a jihar Ribas .
“Amma bayan mun kai rahoto ga jami’an tsaro, sun gano cewa abin ya auku ne a jihar Ribas.”
Hukumar ta fara gudanar da cikakken bincike kan zargin wanda da zarar an gama binciken za ta sanar kan abin da ake ciki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp