• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin Yin Katsa Landan Ba Zai Dakile Ci Gaban Yankin HK Ba

by CGTN Hausa
2 years ago
HK

Kamar dai yadda aka yi tsammani, bayan majalissar dokokin HK ta zartas da kudurin dokar tsaron kasa da gagarumin rinjaye a baya bayan nan, ta kuma cimma nasarar kammala sashe na 23, na dokar gudanarwar yankin na musamman na Sin a ranar 19 ga watan nan, wasu sassa daga kasashen yamma sun zabura, wajen fara sukar wannan mataki, suna masu cewa hanya ce ta dakushe ‘yancin bil adama, kana wasu sun rika nuna shakku, game da yanayin da yankin na HK zai shiga ta fuskar hada hadar kasuwanci.

Amma abun tambaya a nan shi ne, shin wajibi ne a samar da wannan doka ta tsaro? Kuma mene ne ma’anarta ga yankin HK? Alal hakika, zarge-zarge, da kazafi da wadancan sassa suka yiwa Sin ba su da tushe ko makama. Kawai dai akwai wasu mutane a kasashen yamma, dake gudanar da wasan kwaikwayon siyasa da suka saba.

  • Yadda Dimokaradiyya Ke Aiki A Kasar Sin
  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2

Ya zuwa yau, mutane sun kara fahimtar wajibcin wannan doka ta tsaron kasa, la’akari da yamutsin da yankin HK ya sha fama da shi mai nasaba da yunkurin “samun ‘yancin kai”, da tashin hankalin da ya biyo bayan hakan, yayin gyaran dokokin jagorancin yankin.

A shekarar 2020 ne aka tsara dokar tsaron kasa ta yankin HK, aka kuma aiwatar da ita, wadda ta zama ginshikin samun wadata da daidaito a yankin. Yanzu haka shekaru 3 sun shude bayan wannan ci gaba, kuma tuni yankin HK ya sauya daga wurin da ya sha fama da tashe tashen hankula, zuwa wuri mai cikakken tsarin jagoranci da walwala. To sai dai kuma a daya hannun, kalubalen tsaron kasa da yankin ke fuskanta har yanzu yana da sarkakiya da tsanani.

Wannan doka ta tsaron kasa ta HK, da sauran dokokin da ake aiwatarwa a yankin na musamman na Sin, ba su kai ga wadatarwa wajen shawo kan dukkanin dabi’u, da ayyuka dake iya haifar da barazana ga tsaron kasa ba. Zartas da wannan doka ta yankin HK a wannan karo, na da nasaba da aiwatar da kudurorin tsaron kasa na HK, da cike gibin manufar tabbatar da tsaro a HK, da tabbatar da wanzuwar daidaito na dogon lokaci a HK, da ma cimma nasarar gudanar da manufar nan ta “kasa daya tsarin mulki biyu” bisa daidaito.  (Mai fassara: Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani
Daga Birnin Sin

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Next Post
amurka

“Taron Koli Na Demokuradiyya” Da Amurka Ke Gudanarwa Na Cike Da Manufunci Da Girman Kai

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.