A ranar 20 ga wata, Chen Xu, jakadan kasar Sin a ofishin MDD dake birnin Geneva da sauran hukumomin kasa da kasa dake kasar Switzerland, ya yi jawabi a taron karo na 55 na kwamitin kare hakkin dan Adam karkashin MDD, a madadin kungiyar abokai masu neman raya harkar kare hakkin dan Adam ta hanyar musayar ra’ayi da hadin kai, inda jami’in na kasar Sin ya jaddada cewa, ya kamata a inganta aikin kare hakkin dan Adam ta hanyar musayar ra’ayi da kokarin hadin gwiwa, kuma kar a mai da hakkin dan Adam wani batu na siyasa, ko kuma fakewa da shi don neman biyan bukatar kai. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp